< Ayuba 2 >

1 Wata rana kuma mala’iku suka sāke kawo kansu gaban Ubangiji, sai Shaiɗan shi ma ya zo tare da su yă nuna kansa a gabansa.
I stalo se opět jednoho dne, že když přišli synové Boží, aby se postavili před Hospodinem, přišel také i Satan mezi ně, aby se postavil před Hospodinem.
2 Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Daga ina ka fito?” Shaiɗan ya amsa wa Ubangiji ya ce, “Daga yawo a duniya ina kai da kawowa a cikinta.”
Tedy řekl Hospodin Satanovi: Odkud jdeš? I odpověděl Satan Hospodinu, řka: Procházel jsem zemi, a obcházel jsem ji.
3 Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ko ka ga bawana Ayuba? A cikin duniya babu wani kamar sa; shi marar laifi ne, adali kuma, mutum ne mai tsoron Allah ba ruwansa da mugunta. Kuma har yanzu bai fasa zama mai aminci ba duk da wahalar da ka sa na bari ka ba shi ba tare da wani dalili ba.”
I řekl Hospodin Satanovi: Spatřil-lis služebníka mého Joba, že není jemu rovného na zemi, že jest muž sprostný a upřímý, bojící se Boha, a varující se zlého, a že po dnes trvá v upřímnosti své, ačkoli jsi ty mne popudil proti němu, abych jej hubil bez příčiny.
4 Shaiɗan ya amsa ya ce, “Fata don fata! Mutum zai iya rabuwa da duk abin da yake da shi domin ransa.
A odpovídaje Satan Hospodinu, řekl: Kůži za kůži, a všecko, což má člověk, dá za sebe samého.
5 Ka ɗan taɓa lafiyar jikinsa ka gani ba shakka zai la’anta ka kana ji kana gani.”
Ale vztáhni nyní ruku svou, a dotkni se kostí jeho, a masa jeho, nebude-liť v oči zlořečiti tobě.
6 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “To, shi ke nan, duk abin da yake da shi yana hannunka, amma kada ka taɓa shi, shi kansa.”
Tedy řekl Hospodin Satanovi: Aj, v moci tvé buď, a však zachovej ho při životu.
7 Sai Shaiɗan ya bar Ubangiji, ya je ya sa wa Ayuba ƙuraje masu zafi a jikinsa daga tafin ƙafafunsa har zuwa kansa.
Protož vyšed Satan od tváři Hospodinovy, ranil Joba nežitem nejhorším, od zpodku nohy jeho až do vrchu hlavy jeho,
8 Sai Ayuba ya ɗauki kaskon tukunya yana ta sosa ƙurajen da shi, yayinda yake zaune cikin toka.
Tak že vzal střepinu, aby se jí drbal, usadiv se v popele.
9 Matarsa ta ce masa, “Har yanzu kana nan da amincinka? Ka la’anta Allah ka mutu!”
I řekla jemu žena jeho: Ještě vždy trváš v své upřímnosti? Zlořeč Bohu a umři.
10 Ya amsa ya ce, “Kina magana kamar wawiya. Alheri kaɗai za mu dinga samu daga Allah ban da wahala?” A cikin wannan duka Ayuba bai yi zunubi ba cikin maganarsa.
Jížto řekl: Mluvíš, jako jedna z bláznivých mluvívá. Dobré-liž jen věci bráti budeme od Boha, zlých pak nebudeme přijímati? V tom ve všem nezhřešil Job rty svými.
11 Lokacin da abokan Ayuba su uku wato, Elifaz mutumin Teman, Bildad mutumin Shuwa, da Zofar mutumin Na’ama suka ji wahalar da ta auka wa Ayuba, sai suka shirya suka bar gidajensu suka je don su ta’azantar da shi.
Když pak uslyšeli tři přátelé Jobovi o všem tom zlém, kteréž přišlo na něj, přišli jeden každý z místa svého: Elifaz Temanský, a Bildad Suchský a Zofar Naamatský, na tom zůstavše spolu, aby přijdouce k němu, politovali ho a těšili jej.
12 Sa’ad da suka gan shi daga nesa, da ƙyar suka gane shi; sai suka fara kuka da ƙarfi, suka yayyaga tufafinsu suka zuba toka a kawunansu,
Kteříž pozdvihše očí svých zdaleka, nepoznali ho. Potom pozdvihše hlasu svého, plakali, a roztrhše jeden každý roucho své, házeli prachem nad hlavy své zhůru.
13 sai suka zauna da shi a ƙasa har kwana bakwai. Ba wanda ya ce masa kome, don sun ga tsananin wahalar da yake ciki.
A seděli s ním na zemi sedm dní a sedm nocí, a žádný k němu nepromluvil slova; nebo viděli, že se velmi rozmohla bolest jeho.

< Ayuba 2 >