< Ayuba 19 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Eyüp şöyle yanıtladı:
2 “Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
“Ne zamana dek beni üzecek, Sözlerinizle ezeceksiniz?
3 Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
On kez oldu beni aşağılıyor, Hiç utanmadan saldırıyorsunuz.
4 In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
Yanlış yola sapmışsam, Bu benim suçum.
5 In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
Kendinizi gerçekten benden üstün görüyor, Utancımı bana karşı kullanıyorsanız,
6 sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
Bilin ki, Tanrı bana haksızlık yaptı, Beni ağıyla kuşattı.
7 “Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
“İşte, ‘Zorbalık bu!’ diye haykırıyorum, ama yanıt yok, Yardım için bağırıyorum, ama adalet yok.
8 Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
Yoluma set çekti, geçemiyorum, Yollarımı karanlığa boğdu.
9 Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
Üzerimden onurumu soydu, Başımdaki tacı kaldırdı.
10 Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
Her yandan yıktı beni, tükendim, Umudumu bir ağaç gibi kökünden söktü.
11 Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
Öfkesi bana karşı alev alev yanıyor, Beni hasım sayıyor.
12 Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
Orduları üstüme üstüme geliyor, Bana karşı rampalar yapıyor, Çadırımın çevresinde ordugah kuruyorlar.
13 “Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
“Kardeşlerimi benden uzaklaştırdı, Tanıdıklarım bana büsbütün yabancılaştı.
14 Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
Akrabalarım uğramaz oldu, Yakın dostlarım beni unuttu.
15 Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
Evimdeki konuklarla hizmetçiler Beni yabancı sayıyor, Garip oldum gözlerinde.
16 Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
Kölemi çağırıyorum, yanıtlamıyor, Dil döksem bile.
17 Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
Soluğum karımı tiksindiriyor, Kardeşlerim benden iğreniyor.
18 Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
Çocuklar bile beni küçümsüyor, Ayağa kalksam benimle eğleniyorlar.
19 Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
Bütün yakın dostlarım benden iğreniyor, Sevdiklerim yüz çeviriyor.
20 Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
Bir deri bir kemiğe döndüm, Ölümün eşiğine geldim.
21 “Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
“Ey dostlarım, acıyın bana, siz acıyın, Çünkü Tanrı'nın eli vurdu bana.
22 Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
Neden Tanrı gibi siz de beni kovalıyor, Etime doymuyorsunuz?
23 “Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
“Keşke şimdi sözlerim yazılsa, Kitaba geçseydi,
24 a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
Demir kalemle, kurşunla Sonsuza dek kalsın diye kayaya kazılsaydı!
25 Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
Oysa ben kurtarıcımın yaşadığını, Sonunda yeryüzüne geleceğini biliyorum.
26 Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
Derim yok olduktan sonra, Yeni bedenimle Tanrı'yı göreceğim.
27 Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
O'nu kendim göreceğim, Kendi gözlerimle, başkası değil. Yüreğim bayılıyor bağrımda!
28 “In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
Eğer, ‘Sıkıntının kökü onda olduğu için Onu kovalım’ diyorsanız,
29 sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”
Kılıçtan korkmalısınız, Çünkü kılıç cezası öfkeli olur, O zaman adaletin var olduğunu göreceksiniz.”

< Ayuba 19 >