< Ayuba 19 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Y respondió Job, y dijo:
2 “Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
¿Hasta cuándo angustiaréis mi alma: y me moleréis con palabras?
3 Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
Ya me habéis avergonzado diez veces: no tenéis vergüenza de afrentarme.
4 In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
Sea así, que de cierto yo haya errado: conmigo se quedará mi yerro.
5 In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
Mas si vosotros os engrandeciereis contra mí, y redarguyereis contra mí mi oprobrio:
6 sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
Sabéd ahora, que Dios, me trastornó, y trajo al derredor su red sobre mí.
7 “Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
He aquí, yo clamaré agravio, y no seré oído: daré voces, y no habrá juicio.
8 Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
Cercó de vallado mi camino, y no pasaré; y sobre mis veredas puso tinieblas.
9 Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
Quitóme mi honra, y quitó la corona de mi cabeza.
10 Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
Arrancóme al derredor, y me fui; e hizo ir, como de un árbol, mi esperanza.
11 Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
E hizo inflamar contra mí su furor; y contóme a sí entre sus enemigos.
12 Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
Vinieron sus ejércitos a una, y trillaron sobre mí su camino; y asentaron campo en derredor de mi tienda.
13 “Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
Mis hermanos hizo alejar de mí, y mis conocidos ciertamente se extrañaron de mí.
14 Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
Mis parientes se detuvieron; y mis conocidos se olvidaron de mí.
15 Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
Los moradores de mi casa, y mis criadas, me tuvieron por extraño: extraño fui yo en sus ojos.
16 Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
Llamé a mi siervo, y no respondió; de mi propia boca le rogaba.
17 Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
Mi aliento fue hecho extraño a mi mujer, y por los hijos de mi vientre le rogaba.
18 Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
Aun los muchachos me menospreciaron: en levantándome, luego hablaban contra mí.
19 Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
Todos los varones de mi secreto me aborrecieron; y los que yo amaba, se tornaron contra mí.
20 Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
Mi hueso se pegó a mi piel y a mi carne, y he escapado con el cuero de mis dientes.
21 “Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
¡Oh vosotros mis amigos tenéd compasión de mí, tenéd compasión de mí! porque la mano de Dios me ha tocado.
22 Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
¿Por qué me perseguís como Dios, y no os hartáis de mis carnes?
23 “Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
¿Quién diese ahora que mis palabras fuesen escritas? ¿Quién diese que se escribiesen en un libro?
24 a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
¿Qué con cincel de hierro y con plomo fuesen en piedra esculpidas para siempre?
25 Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
Yo sé que mi Redentor vive, y que al fin se levantará sobre el polvo.
26 Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
Y después, desde este mi roto cuero, y desde mi propia carne tengo de ver a Dios:
27 Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
Al cual yo tengo de ver por mí, y mis ojos le han de ver, y no otro, [aunque] mis riñones se consuman dentro de mí.
28 “In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
¿Por qué no decís: Por qué le perseguimos? pues que la raíz del negocio se halla en mí.
29 sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”
Teméd a vosotros delante de la espada; porque la ira de la espada de las maldades viene: porque sepáis que hay juicio.

< Ayuba 19 >