< Ayuba 19 >
2 “Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
¿Hasta cuándo afligen mi alma y me muelen con palabras?
3 Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
Ya me insultaron diez veces. ¿No se avergüenzan de ultrajarme?
4 In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
Si en verdad yo erré, mi error recae sobre mí.
5 In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
Pero si ustedes se engrandecen contra mí, y alegan mi oprobio contra mí,
6 sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
sepan que ʼElohim me trastornó y me envolvió en su red.
7 “Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
Ciertamente grito: ¡Violencia! Y no se me escucha. Doy voces, y no hay justicia.
8 Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
Él bloqueó mi camino para que no pase. Puso oscuridad sobre mi senda.
9 Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
Me despojó de mi honor y quitó la corona de mi cabeza.
10 Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
Me destroza por todos lados y perezco. Arrancó mi esperanza como un árbol.
11 Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
Su ira se encendió contra mí. Me considera su enemigo.
12 Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
Llegaron sus tropas unidas, se atrincheran contra mí y acamparon alrededor de mi vivienda.
13 “Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
Alejó a mis hermanos de mí. Mis conocidos, como extraños, se apartaron de mí.
14 Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
Me fallaron mis parientes, me olvidan mis amigos.
15 Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
Los que viven en mi casa y mis esclavas me miran como extraño. Soy forastero ante ellos.
16 Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
Llamo a mi esclavo, y no responde. Con mi propia boca tengo que rogarle.
17 Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
Mi aliento fue repulsivo a mi esposa y odioso ante mis propios hermanos.
18 Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
Hasta los niños me desprecian, y al levantarme hablan contra mí.
19 Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
Todos mis amigos íntimos me aborrecen. Los que yo amaba se volvieron contra mí.
20 Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
Mi piel y mi carne se pegan a mis huesos, y quedé solo con la piel de mis dientes.
21 “Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
Ustedes, amigos míos, tengan compasión de mí. Porque me golpeó la mano de ʼElohim.
22 Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
¿Por qué me persiguen como ʼElohim, y no se sacian de escarnecerme?
23 “Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
¡Ojalá mis palabras fueran escritas! ¡Ojalá fueran escritas en un rollo!
24 a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
¡Que fueran talladas con cincel de hierro y plomo para siempre en la roca!
25 Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
Yo sé que mi Redentor vive, y al fin se levantará sobre el polvo,
26 Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
Después de deshecha mi piel, en mi carne veré a ʼElohim,
27 Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
a Quien veré por mí mismo. Mis ojos lo verán, y no los de otro. Mi corazón desfallece dentro de mí.
28 “In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
Porque si la raíz de mi situación está en mí mismo, entonces, ¿por qué dicen ustedes: Persigámoslo?
29 sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”
¡Teman ustedes ante la espada! Porque llenos de ira están los castigos de la espada, para que sepan que hay un juicio.