< Ayuba 19 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Porém Jó respondeu dizendo:
2 “Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
Até quando atormentareis minha alma, e me quebrantareis com palavras?
3 Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
Já dez vezes me humilhastes; não tendes vergonha em me maltratar.
4 In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
Mesmo se eu tiver errado, meu erro cabe apenas a mim.
5 In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
Visto que vos exaltais contra mim, e contra mim usais minha desgraça,
6 sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
Sabei, pois, que foi Deus que me transtornou, e [com] sua rede me cercou.
7 “Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
Eis que eu clamo: Violência! Porém não sou respondido; grito, porém não há justiça.
8 Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
Ele entrincheirou meu caminho, de modo que não consigo passar; e pôs trevas sobre minhas veredas.
9 Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
Ele me despojou de minha honra, e tirou a coroa de minha cabeça.
10 Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
Ele me derrubou por todos os lados, e pereço; e arrancou minha esperança como a uma árvore.
11 Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
E fez inflamar contra mim sua ira, e me considerou para consigo como a [um de] seus inimigos.
12 Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
Juntas vieram suas tropas; prepararam contra mim seu caminho, e se acamparam ao redor de minha tenda.
13 “Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
Ele afastou meus irmãos para longe de mim; e os que me conheciam agora me estranham.
14 Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
Meus parentes [me] deixaram, e meus conhecidos se esqueceram de mim.
15 Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
Os moradores de minha casa e minhas servas me tiveram por estranho; estrangeiro me tornei em seus olhos.
16 Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
Chamei a meu servo, e ele não respondeu; de minha própria boca eu lhe suplicava.
17 Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
Meu hálito é estranho à minha mulher, e sou repugnante aos filhos de minha mãe.
18 Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
Até os meninos me desprezam; quando eu me levanto, falam contra mim.
19 Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
Todos os meus amigos próximos me abominam; e [até] aqueles que eu amava se viraram contra mim.
20 Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
Meus ossos se grudaram à minha pele e à minha carne; e escapei [só] com a pele de meus dentes.
21 “Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
Compadecei-vos de mim, meus amigos, compadecei-vos de mim; pois a mão de Deus me tocou.
22 Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
Por que vós me perseguis como Deus, e não vos fartais de minhas carne?
23 “Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
Ah se minhas palavras fossem escritas! Ah se fossem escritas em um livro!
24 a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
Que com ponta de ferro e com chumbo fossem esculpidas em pedra para sempre!
25 Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
Pois eu sei que meu Redentor vive, e ao fim se levantará sobre a terra;
26 Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
E mesmo depois de consumida minha pele, então em minha carne verei a Deus;
27 Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
Ao qual eu verei para mim, e meus olhos [o] verão, e não outro. [Isto é o que] minhas entranhas anseiam dentro de mim.
28 “In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
Se disserdes: Como o perseguiremos? Pois a raiz do problema se acha em mim,
29 sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”
Temei vós mesmos a espada; pois furor [há nos] castigos pela espada; para que [assim] saibais que [haverá] julgamento.

< Ayuba 19 >