< Ayuba 19 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Respondens autem Job, dixit:
2 “Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
[Usquequo affligitis animam meam, et atteritis me sermonibus?
3 Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
En decies confunditis me, et non erubescitis opprimentes me.
4 In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
Nempe etsi ignoravi, mecum erit ignorantia mea.
5 In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
At vos contra me erigimini, et arguitis me opprobriis meis.
6 sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
Saltem nunc intelligite quia Deus non æquo judicio afflixerit me, et flagellis suis me cinxerit.
7 “Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
Ecce clamabo, vim patiens, et nemo audiet; vociferabor, et non est qui judicet.
8 Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
Semitam meam circumsepsit, et transire non possum: et in calle meo tenebras posuit.
9 Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
Spoliavit me gloria mea, et abstulit coronam de capite meo.
10 Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
Destruxit me undique, et pereo: et quasi evulsæ arbori abstulit spem meam.
11 Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
Iratus est contra me furor ejus, et sic me habuit quasi hostem suum.
12 Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
Simul venerunt latrones ejus, et fecerunt sibi viam per me, et obsederunt in gyro tabernaculum meum.
13 “Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
Fratres meos longe fecit a me, et noti mei quasi alieni recesserunt a me.
14 Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
Dereliquerunt me propinqui mei, et qui me noverant obliti sunt mei.
15 Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
Inquilini domus meæ et ancillæ meæ sicut alienum habuerunt me, et quasi peregrinus fui in oculis eorum.
16 Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
Servum meum vocavi, et non respondit: ore proprio deprecabar illum.
17 Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
Halitum meum exhorruit uxor mea, et orabam filios uteri mei.
18 Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
Stulti quoque despiciebant me: et cum ab eis recessissem, detrahebant mihi.
19 Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
Abominati sunt me quondam consiliarii mei, et quem maxime diligebam, aversatus est me.
20 Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
Pelli meæ, consumptis carnibus, adhæsit os meum, et derelicta sunt tantummodo labia circa dentes meos.
21 “Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
Miseremini mei, miseremini mei saltem vos, amici mei, quia manus Domini tetigit me.
22 Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
Quare persequimini me sicut Deus, et carnibus meis saturamini?
23 “Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
Quis mihi tribuat ut scribantur sermones mei? quis mihi det ut exarentur in libro
24 a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
stylo ferreo et plumbi lamina, vel celte sculpantur in silice?
25 Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
Scio enim quod redemptor meus vivit, et in novissimo die de terra surrecturus sum:
26 Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
et rursum circumdabor pelle mea, et in carne mea videbo Deum meum:
27 Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
quem visurus sum ego ipse, et oculi mei conspecturi sunt, et non alius: reposita est hæc spes mea in sinu meo.
28 “In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
Quare ergo nunc dicitis: Persequamur eum, et radicem verbi inveniamus contra eum?
29 sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”
Fugite ergo a facie gladii, quoniam ultor iniquitatum gladius est: et scitote esse judicium.]

< Ayuba 19 >