< Ayuba 19 >
2 “Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
汝ら我心をなやまし 言語をもて我を打くだくこと何時までぞや
3 Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
なんぢら已に十次も我を辱しめ我を惡く待ひてなほ愧るところ無し
4 In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
假令われ眞に過ちたらんもその過は我の身に止れり
5 In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
なんぢら眞に我に向ひて誇り我身に羞べき行爲ありと證するならば
6 sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
神われを虐げその網羅をもて我と包みたまへりと知るべし
7 “Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
我虐げらるると叫べども答なく 呼はり求むれども審理なし
8 Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
彼わが路の周圍に垣を結めぐらして逾る能はざらしめ 我が行く途に黒暗を蒙むらしめ
9 Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
わが光榮を褫ぎわが冠冕を首より奪ひ
10 Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
四方より我を毀ちて失しめ 我望を樹のごとくに根より拔き
11 Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
我にむかひて震怒を燃し 我を敵の一人と見たまへり
12 Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
その軍旅ひとしく進み途を高くして我に攻寄せ わが天幕の周圍に陣を張り
13 “Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
彼わが兄弟等をして遠くわれを離れしめたまへり 我を知る人々は全く我に疎くなりぬ
14 Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
わが親戚は往來を休め わが朋友はわれを忘れ
15 Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
わが家に寄寓る者およびわが婢等は我を見て外人のごとくす 我かれらの前にては異國人のごとし
16 Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
われわが僕を喚べどもこたへず 我口をもて彼に請はざるを得ざるなり
17 Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
わが氣息はわが妻に厭はれ わが臭氣はわが同胎の子等に嫌はる
18 Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
童子等さへも我を侮どり 我起あがれば則ち我を嘲ける
19 Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
わが親しき友われを惡みわが愛したる人々ひるがへりてわが敵となれり
20 Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
わが骨はわが皮と肉とに貼り 我は僅に齒の皮を全うして逃れしのみ
21 “Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
わが友よ汝等われを恤れめ 神の手われを撃り
22 Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
汝らなにとて神のごとくして我を攻め わが肉に饜ことなきや
23 “Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
望むらくは我言の書留られんことを 望むらくは我言書に記されんことを
24 a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
望むらくは鐡の筆と鉛とをもて之を永く磐石に鐫つけおかんことを
25 Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
われ知る我を贖ふ者は活く 後の日に彼かならず地の上に立ん
26 Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
わがこの皮この身の朽はてん後われ肉を離れて神を見ん
27 Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
我みづから彼を見たてまつらん 我目かれを見んに識らぬ者のごとくならじ 我が心これを望みて焦る
28 “In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
なんぢら若われら如何に彼を攻めんかと言ひ また事の根われに在りと言ば
29 sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”
劍を懼れよ 忿怒は劍の罰をきたらす 斯なんぢら遂に審判のあるを知ん