< Ayuba 19 >
But Job answered and said:
2 “Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
How long will ye vex my soul, And break me in pieces with words?
3 Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
These ten times have ye reviled me; Without shame do ye stun me!
4 In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
And be it, indeed, that I have erred, My error abideth with myself.
5 In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
Since, indeed, ye magnify yourselves against me, And plead against me my reproach,
6 sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
Know then that it is God who hath brought me low; He hath encompassed me with his net.
7 “Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
Behold, I complain of wrong, but receive no answer; I cry aloud, but obtain no justice.
8 Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
He hath fenced up my way, so that I cannot pass, And hath set darkness in my paths.
9 Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
He hath stripped me of my glory, And taken the crown from my head.
10 Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
He hath destroyed me on every side, and I am gone! He hath torn up my hope like a tree.
11 Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
He kindleth his anger against me, And counteth me as his enemy.
12 Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
His troops advance together against me; They throw up for themselves a way to me, And encamp around my dwelling.
13 “Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
My brethren he hath put far from me, And my acquaintance are wholly estranged from me.
14 Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
My kinsfolk have forsaken me, And my bosom friends have forgotten me.
15 Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
The foreigners of my house, yea, my own maid-servants, regard me as a stranger; I am an alien in their eyes.
16 Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
I call my servant, and he maketh no answer; With my own mouth do I entreat him.
17 Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
My breath is become strange to my wife, And my prayers also to my own mother's sons.
18 Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
Even young children despise me; When I rise up, they speak against me.
19 Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
All my bosom friends abhor me, And they whom I loved are turned against me.
20 Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
My bones cleave to my flesh and my skin, And I have scarcely escaped with the skin of my teeth.
21 “Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
Have pity upon me, O ye my friends! have pity upon me; For the hand of God hath smitten me!
22 Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
Why do ye persecute me like God, And are not satisfied with my flesh?
23 “Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
O that my words were now written! O that they were marked down in a scroll!
24 a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
That with an iron pen, and with lead, They were engraven upon the rock for ever!
25 Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
Yet I know that my Vindicator liveth, And will hereafter stand up on the earth;
26 Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
And though with my skin this body be wasted away, Yet without my flesh shall I see God.
27 Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
Yea, I shall see him my friend; My eyes shall behold him, and not another: For this, my soul panteth within me.
28 “In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
Since ye say, “How may we persecute him, And find grounds of accusation against him?”
29 sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”
Be ye afraid of the sword! For malice is a crime for the sword; That ye may know that judgment cometh.