< Ayuba 19 >
Then Job answered, and said,
2 “Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
How long will ye vex my soul, and break me in pieces with words?
3 Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
These ten times ye have reproached me. Ye are not ashamed that ye deal hardly with me.
4 In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
And be it indeed that I have erred, my error remains with myself.
5 In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
If indeed ye will magnify yourselves against me, and plead against me my reproach,
6 sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
know now that God has subverted me, and has encompassed me with his net.
7 “Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
Behold, I cry out of wrong, but I am not heard. I cry for help, but there is no justice.
8 Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
He has walled up my way that I cannot pass, and has set darkness in my paths.
9 Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
He has stripped me of my glory, and taken the crown from my head.
10 Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
He has broken me down on every side, and I am gone. And he has plucked up my hope like a tree.
11 Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
He has also kindled his wrath against me. And he considers me to him as his adversaries.
12 Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
His troops come on together, and cast up their way against me, and encamp round about my tent.
13 “Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
He has put my brothers far from me, and my acquaintances are wholly estranged from me.
14 Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
My kinsfolk have failed, and my familiar friends have forgotten me.
15 Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
Those who dwell in my house, and my maids, reckon me for a stranger; I am an alien in their sight.
16 Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
I call to my servant, and he gives me no answer. I entreat him with my mouth.
17 Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
My breath is strange to my wife, and my supplication to the sons of my own mother.
18 Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
Even young children despise me. If I arise, they speak against me.
19 Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
All my familiar friends abhor me, and those whom I loved are turned against me.
20 Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
My bone cleaves to my skin and to my flesh, and I have escaped with the skin of my teeth.
21 “Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
Have pity upon me, have pity upon me, O ye my friends, for the hand of God has touched me.
22 Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
Why do ye persecute me as God, and are not satisfied with my flesh?
23 “Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
O that my words were now written! O that they were inscribed in a book,
24 a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
that they were engraved in the rock forever with an iron pen and lead!
25 Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
But as for me I know that my Redeemer lives, and at last he will stand up upon the earth.
26 Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
And after my skin, this body, is destroyed, then outside my flesh I shall see God,
27 Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
whom I, even I, shall see on my side, and my eyes shall behold, and not as a stranger. My heart is consumed within me.
28 “In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
If ye say, How we will persecute him! And that the root of the matter is found in me,
29 sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”
be ye afraid of the sword. For wrath brings the punishments of the sword, that ye may know there is a judgment.