< Ayuba 19 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Job antwoordde, en sprak:
2 “Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
Hoe lang nog blijft gij mij krenken, En mij onder woorden verpletteren?
3 Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
Tien keer beschimpt gij mij reeds, En kwelt gij mij schaamteloos.
4 In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
Zelfs al had ik mij werkelijk misdragen, Dan raakt het wangedrag mij alleen;
5 In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
Gij mist het recht, een grote mond tegen mij op te zetten, Mijn schande mij te verwijten!
6 sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
Erkent toch eindelijk, dat God mij kastijdt, En mij in zijn net heeft verstrikt!
7 “Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
Zie, ik roep: "Geweld!" maar vind geen verhoring, Ik roep om hulp: mij geschiedt geen recht!
8 Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
Hij heeft mijn weg versperd: ik kan niet voorbij, En duisternis op mijn paden gelegd;
9 Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
Mijn eer heeft Hij mij ontroofd, De kroon mij van het hoofd gerukt.
10 Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
Hij heeft mij van alle kant ondermijnd: en daar ga ik heen; Mijn hoop ontworteld als een boom,
11 Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
Zijn gramschap tegen mij laten woeden, Mij als zijn vijand behandeld.
12 Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
Als één man rukken zijn benden aan, En banen hun weg naar mij heen; Ze legeren zich rond mijn tent, Ze zijn zonder genade!
13 “Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
Mijn broeders houden zich verre van mij, Mijn bekenden zijn vreemden voor mij;
14 Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
Mijn verwanten verdwenen, Mijn gasten zijn mij vergeten.
15 Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
Mijn slavinnen zien mij aan voor een vreemde, Ik ben een onbekende voor haar;
16 Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
Ik roep mijn slaaf: hij geeft mij geen antwoord, Zelfs al smeek ik er om.
17 Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
Mijn vrouw walgt van mijn adem, En ik stink voor mijn zonen;
18 Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
Zelfs de kinderen minachten mij, En brutaliseren mij, als ik optreed.
19 Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
Al mijn getrouwen verafschuwen mij, Die ik liefhad, keren zich van mij af;
20 Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
Mijn vlees teert weg in mijn huid Met mijn tanden knaag ik mijn beenderen af.
21 “Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
Erbarming, erbarming: gij tenminste, mijn vrienden, Want de hand van God heeft mij geraakt;
22 Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
Waarom mij als een hert vervolgen, Nooit verzadigd aan mijn vlees!
23 “Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
O, werden mijn woorden opgeschreven, Opgetekend in een boek,
24 a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
Met een stift van ijzer en lood Voor eeuwig op een rots gegrift:
25 Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
Ik weet, dat mijn Verlosser leeft, En ten leste op de aarde verschijnt;
26 Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
Dat ik mij zal oprichten achter mijn huid, En van mijn vlees uit, God zal aanschouwen!
27 Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
Ja, ik zal Hem aanschouwen, Mijn ogen zullen Hem zien, maar niet meer als vijand; Mijn nieren smachten in mijn schoot,
28 “In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
En wanneer gij dan zegt: Hoe vervolgen we hem, Welk voorwendsel zullen we tegen hem vinden;
29 sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”
Ducht dan het zwaard voor uzelf, Want dan zal de Gramschap de bozen verdelgen! Om te weten, of er gerechtigheid is!

< Ayuba 19 >