< Ayuba 18 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Y RESPONDIÓ Bildad Suhita, y dijo:
2 “Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
¿Cuándo pondréis fin á las palabras? Entended, y después hablemos.
3 Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
¿Por qué somos tenidos por bestias, y en vuestros ojos somos viles?
4 Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
Oh tú, que despedazas tu alma con tu furor, ¿será dejada la tierra por tu causa, y serán traspasadas de su lugar las peñas?
5 “An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
Ciertamente la luz de los impíos será apagada, y no resplandecerá la centella de su fuego.
6 Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
La luz se oscurecerá en su tienda, y apagaráse sobre él su lámpara.
7 Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
Los pasos de su pujanza serán acortados, y precipitarálo su mismo consejo.
8 Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
Porque red será echada en sus pies, y sobre red andará.
9 Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
Lazo prenderá [su] calcañar: afirmaráse la trampa contra él.
10 An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
Su cuerda está escondida en la tierra, y su torzuelo sobre la senda.
11 Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
De todas partes lo asombrarán temores, y haránle huir desconcertado.
12 Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
Su fuerza será hambrienta, y á su lado estará aparejado quebrantamiento.
13 Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
El primogénito de la muerte comerá los ramos de su piel, y devorará sus miembros.
14 An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
Su confianza será arrancada de su tienda, y harále esto llevar al rey de los espantos.
15 Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
En su tienda morará como si no fuese suya: piedra azufre será esparcida sobre su morada.
16 Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
Abajo se secarán sus raíces, y arriba serán cortadas sus ramas.
17 An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
Su memoria perecerá de la tierra, y no tendrá nombre por las calles.
18 An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
De la luz será lanzado á las tinieblas, y echado fuera del mundo.
19 Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
No tendrá hijo ni nieto en su pueblo, ni quien [le] suceda en sus moradas.
20 Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
Sobre su día se espantarán los por venir, como ocupó el pavor á los que fueron antes.
21 Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”
Ciertamente tales son las moradas del impío, y este será el lugar del que no conoció á Dios.

< Ayuba 18 >