< Ayuba 18 >
1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Então Bildade, o suíta, respondeu, dizendo:
2 “Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
Quando é que dareis fim às palavras? Prestai atenção, e então falaremos.
3 Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
Por que somos considerados animais, e tolos em vossos olhos?
4 Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
Ó tu, que despedaças tua alma com tua ira; será a terra abandonada por tua causa, e será movida a rocha de seu lugar?
5 “An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
Na verdade, a luz dos perverso se apagará, e a faísca de seu fogo não brilhará.
6 Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
A luz se escurecerá em sua tenda, e sua lâmpada sobre ele se apagará.
7 Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
Os seus passos fortes serão encurtados, e seu [próprio] intento o derrubará.
8 Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
Pois será lançado à rede pelos seus [próprios] pés, e sobre fios enredados andará.
9 Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
Laço o pegará pelo calcanhar; a armadilha o prenderá.
10 An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
Uma corda lhe está escondida debaixo da terra, e uma armadilha para ele está no caminho.
11 Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
Assombros o espantarão ao redor, e o farão correr por onde seus passos forem.
12 Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
Sua força se tornará em fome, e a perdição está pronta ao seu lado.
13 Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
Partes de sua pele serão consumidas; o primogênito da morte devorará os membros de seu corpo.
14 An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
Será arrancado de sua tenda em que confiava, e será levado ao rei dos assombros.
15 Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
Em sua tenda morará o que não é seu; enxofre se espalhará sobre a sua morada.
16 Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
Por debaixo suas raízes se secarão, e por cima seus ramos serão cortados.
17 An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
Sua memória perecerá da terra, e não terá nome pelas ruas.
18 An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
Será lançado da luz para as trevas, e expulso será do mundo.
19 Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
Não terá filho nem neto entre seu povo, nem sobrevivente em suas moradas.
20 Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
Os do ocidente se espantarão com o seu dia, e os do oriente ficarão horrorizados.
21 Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”
Assim são as moradas do perverso, e este é o lugar [daquele que] não reconhece a Deus.