< Ayuba 18 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Respondens autem Baldad Suhites, dixit:
2 “Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
[Usque ad quem finem verba jactabitis? intelligite prius, et sic loquamur.
3 Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
Quare reputati sumus ut jumenta, et sorduimus coram vobis?
4 Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
Qui perdis animam tuam in furore tuo, numquid propter te derelinquetur terra, et transferentur rupes de loco suo?
5 “An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
Nonne lux impii extinguetur, nec splendebit flamma ignis ejus?
6 Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
Lux obtenebrescet in tabernaculo illius, et lucerna quæ super eum est extinguetur.
7 Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
Arctabuntur gressus virtutis ejus, et præcipitabit eum consilium suum.
8 Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
Immisit enim in rete pedes suos, et in maculis ejus ambulat.
9 Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
Tenebitur planta illius laqueo, et exardescet contra eum sitis.
10 An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
Abscondita est in terra pedica ejus, et decipula illius super semitam.
11 Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
Undique terrebunt eum formidines, et involvent pedes ejus.
12 Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
Attenuetur fame robur ejus, et inedia invadat costas illius.
13 Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
Devoret pulchritudinem cutis ejus; consumat brachia illius primogenita mors.
14 An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
Avellatur de tabernaculo suo fiducia ejus, et calcet super eum, quasi rex, interitus.
15 Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
Habitent in tabernaculo illius socii ejus qui non est; aspergatur in tabernaculo ejus sulphur.
16 Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
Deorsum radices ejus siccentur: sursum autem atteratur messis ejus.
17 An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
Memoria illius pereat de terra, et non celebretur nomen ejus in plateis.
18 An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
Expellet eum de luce in tenebras, et de orbe transferet eum.
19 Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
Non erit semen ejus, neque progenies in populo suo, nec ullæ reliquiæ in regionibus ejus.
20 Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
In die ejus stupebunt novissimi, et primos invadet horror.
21 Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”
Hæc sunt ergo tabernacula iniqui, et iste locus ejus qui ignorat Deum.]

< Ayuba 18 >