< Ayuba 18 >
1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Da antwortete Bildad von Suah und sprach:
2 “Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
Wann wollt ihr der Reden ein Ende machen? Merkt doch; darnach wollen wir reden.
3 Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
Warum werden wir geachtet wie Vieh und sind so unrein vor euren Augen?
4 Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
Willst du vor Zorn bersten? Meinst du, daß um deinetwillen die Erde verlassen werde und der Fels von seinem Ort versetzt werde?
5 “An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
Und doch wird das Licht der Gottlosen verlöschen, und der Funke seines Feuers wird nicht leuchten.
6 Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
Das Licht wird finster werden in seiner Hütte, und seine Leuchte über ihm verlöschen.
7 Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
Seine kräftigen Schritte werden in die Enge kommen, und sein Anschlag wird ihn fällen.
8 Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
Denn er ist mit seinen Füßen in den Strick gebracht und wandelt im Netz.
9 Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
Der Strick wird seine Ferse halten, und die Schlinge wird ihn erhaschen.
10 An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
Sein Strick ist gelegt in die Erde, und seine Falle auf seinem Gang.
11 Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
Um und um wird ihn schrecken plötzliche Furcht, daß er nicht weiß, wo er hinaus soll.
12 Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
Hunger wird seine Habe sein, und Unglück wird ihm bereit sein und anhangen.
13 Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
Die Glieder seines Leibes werden verzehrt werden; seine Glieder wird verzehren der Erstgeborene des Todes.
14 An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
Seine Hoffnung wird aus seiner Hütte ausgerottet werden, und es wird ihn treiben zum König des Schreckens.
15 Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
In seiner Hütte wird nichts bleiben; über seine Stätte wird Schwefel gestreut werden.
16 Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
Von unten werden verdorren seine Wurzeln, und von oben abgeschnitten seine Zweige.
17 An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
Sein Gedächtnis wird vergehen in dem Lande, und er wird keinen Namen haben auf der Gasse.
18 An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
Er wird vom Licht in die Finsternis vertrieben und vom Erdboden verstoßen werden.
19 Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
Er wird keine Kinder haben und keine Enkel unter seinem Volk; es wird ihm keiner übrigbleiben in seinen Gütern.
20 Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
Die nach ihm kommen, werden sich über seinen Tag entsetzen; und die vor ihm sind, wird eine Furcht ankommen.
21 Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”
Das ist die Wohnung des Ungerechten; und dies ist die Stätte des, der Gott nicht achtet.