< Ayuba 18 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Bildad von Suah antwortete und sprach:
2 “Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
Wie lange wollt ihr diese Wortjagd treiben? Kommt zu Verstand, hernach wollen wir reden!
3 Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
Weswegen werden wir dem Vieh gleichgeachtet, gelten für vernagelt in euren Augen?
4 Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
Du, der sich in seinem Grimme selbst zerfleischt, - soll um deinetwillen die Erde entvölkert werden, und der Fels von seiner Stelle rücken?
5 “An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
Jawohl erlischt der Gottlosen Licht, und seines Feuers Flamme leuchtet nicht.
6 Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
Das Licht verfinstert sich in seinem Zelt, und seine Leuchte über ihm erlischt.
7 Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
Seine rüstigen Schritte werden kurz, sein eigner Anschlag stürzt ihn ins Verderben.
8 Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
Denn ins Netz wird er getrieben mit seinen Füßen und über Flechtwerk wandelt er dahin.
9 Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
Die Ferse packt ein Fallstrick, fest hält ihn die Schlinge.
10 An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
An der Erde ist der Strick für ihn versteckt, und die Falle für ihn auf dem Pfade.
11 Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
Ringsum ängstigen ihn Schrecknisse und scheuchen ihn auf Schritt und Tritt.
12 Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
Es hungert nach ihm das Unheil, und das Verderben klammert sich an seine Seite.
13 Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
Es frißt die Glieder seines Leibes, es frißt seine Glieder der Erstgeborene des Todes.
14 An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
Er wird herausgerissen aus seinem Zelt, auf das er vertraute: es treibt ihn hin zum Könige der Schrecken.
15 Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
In seinem Zelte wohnt, was ihm nicht angehört, auf seine Wohnstätte wird Schwefel gestreut.
16 Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
Unten verdorren seine Wurzeln, und oben verwelkt sein Gezweig.
17 An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
Sein Gedächtnis verschwindet von der Erde, und kein Name bleibt ihm auf der Flur.
18 An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
Man stößt ihn aus dem Licht in Finsternis und treibt ihn weg vom Erdenrund.
19 Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
Nicht Sproß bleibt ihm noch Schoß in seinem Volk, und kein Entronnener ist in seiner Behausung.
20 Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
Oba seines Verhängnistags erstarren die im Westen, und Schauder packt, die im Osten wohnen.
21 Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”
Ja, so ergeht's der Wohnung des Frevlers, und so der Stätte dessen, der sich um Gott nicht kümmerte!

< Ayuba 18 >