< Ayuba 18 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Bildad de Schuach prit la parole et dit:
2 “Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
Quand mettrez-vous un terme à ces discours? Ayez de l’intelligence, puis nous parlerons.
3 Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
Pourquoi sommes-nous regardés comme des bêtes? Pourquoi ne sommes-nous à vos yeux que des brutes?
4 Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
O toi qui te déchires dans ta fureur, Faut-il, à cause de toi, que la terre devienne déserte? Faut-il que les rochers disparaissent de leur place?
5 “An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
La lumière du méchant s’éteindra, Et la flamme qui en jaillit cessera de briller.
6 Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
La lumière s’obscurcira sous sa tente, Et sa lampe au-dessus de lui s’éteindra.
7 Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
Ses pas assurés seront à l’étroit; Malgré ses efforts, il tombera.
8 Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
Car il met les pieds sur un filet, Il marche dans les mailles,
9 Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
Il est saisi au piège par le talon, Et le filet s’empare de lui;
10 An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
Le cordeau est caché dans la terre, Et la trappe est sur son sentier.
11 Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
Des terreurs l’assiègent, l’entourent, Le poursuivent par derrière.
12 Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
La faim consume ses forces, La misère est à ses côtés.
13 Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
Les parties de sa peau sont l’une après l’autre dévorées, Ses membres sont dévorés par le premier-né de la mort.
14 An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
Il est arraché de sa tente où il se croyait en sûreté, Il se traîne vers le roi des épouvantements.
15 Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
Nul des siens n’habite sa tente, Le soufre est répandu sur sa demeure.
16 Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
En bas, ses racines se dessèchent; En haut, ses branches sont coupées.
17 An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
Sa mémoire disparaît de la terre, Son nom n’est plus sur la face des champs.
18 An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
Il est poussé de la lumière dans les ténèbres, Il est chassé du monde.
19 Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
Il ne laisse ni descendants ni postérité parmi son peuple, Ni survivant dans les lieux qu’il habitait.
20 Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
Les générations à venir seront étonnées de sa ruine, Et la génération présente sera saisie d’effroi.
21 Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”
Point d’autre destinée pour le méchant, Point d’autre sort pour qui ne connaît pas Dieu!

< Ayuba 18 >