< Ayuba 18 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Bildad prit la parole et dit:
2 “Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
Jusqu’à quand ferez-vous assaut de discours? Devenez raisonnables, puis nous pourrons parler.
3 Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
Pourquoi nous considère-t-on comme des brutes? Pourquoi sommes-nous bornés à vos yeux!
4 Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
O toi, qui te déchires toi-même dans ta fureur, est-ce par amour de toi que la terre sera abandonnée et que le rocher changera de place?
5 “An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
Oui certes, la lampe des méchants s’éteint, la flamme de son foyer cesse de briller.
6 Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
La lumière s’obscurcit dans sa tente, son flambeau s’éteint au-dessus de lui.
7 Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
Ses pas, jadis assurés, deviennent hésitants, il est renversé par ses propres projets.
8 Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
Car ses pieds se prennent dans le filet, il chemine sur des rets.
9 Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
Le piège le saisit au talon, le traquenard se referme violemment sur lui.
10 An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
Des entraves lui sont posées secrètement sur le sol, des embûches couvrent la route qu’il suit.
11 Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
De toutes parts les terreurs le poursuivent et font vaciller ses jambes.
12 Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
Sa vigueur dépérit par la faim, la ruine menace ses flancs.
13 Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
Les lambeaux de sa peau deviennent une pâture, ses membres, une proie pour le premier-né de la mort.
14 An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
Il est arraché de la tente où il vivait en sécurité, et poussé entre les bras du roi des épouvantements.
15 Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
Des gens qui ne lui sont de rien se fixent dans sa demeure; une pluie de soufre se répand sur son domaine.
16 Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
Par en bas, ses racines se dessèchent, par en haut, son feuillage se flétrit.
17 An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
Son souvenir s’efface de la terre, et rien ne rappelle son nom dans l’étendue du monde.
18 An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
On le repousse de la lumière dans les ténèbres et on l’expulse de l’univers.
19 Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
Il ne laisse ni lignée, ni postérité, ni aucun survivant dans son habitation.
20 Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
Sa destinée frappe de stupeur ceux de l’Occident et donne le frisson à ceux de l’Orient.
21 Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”
Oui, voilà ce qui attend les demeures du malfaiteur, la résidence de qui ne reconnaît pas Dieu!

< Ayuba 18 >