< Ayuba 18 >
1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Et Bildad, le Shuhite, prit la parole,
2 “Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
« Combien de temps allez-vous chercher les mots? Réfléchissez, et après nous parlerons.
3 Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
Pourquoi sommes-nous comptés comme des animaux, qui sont devenus impurs à vos yeux?
4 Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
Toi qui te déchires dans ta colère, la terre sera-t-elle abandonnée pour vous? Ou bien la pierre sera-t-elle retirée de son emplacement?
5 “An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
« Oui, la lumière des méchants sera éteinte. L'étincelle de son feu ne brillera pas.
6 Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
La lumière sera sombre dans sa tente. Sa lampe au-dessus de lui sera éteinte.
7 Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
Les pas de sa force seront abrégés. Son propre conseil le fera tomber.
8 Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
Car il est jeté dans un filet par ses propres pieds, et il s'égare dans ses mailles.
9 Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
Un piège le saisit par le talon. Un piège va l'attraper.
10 An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
Un nœud coulant est caché pour lui dans le sol, un piège pour lui sur le chemin.
11 Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
Des terreurs l'effraieront de toutes parts, et le poursuivra sur ses talons.
12 Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
Sa force sera affamée. Calamity sera prêt à ses côtés.
13 Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
Les membres de son corps seront dévorés. Le premier-né de la mort dévorera ses membres.
14 An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
Il sera déraciné de la sécurité de sa tente. Il sera amené au roi des terreurs.
15 Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
Dans sa tente habitera ce qui n'est pas à lui. Le soufre sera répandu sur sa demeure.
16 Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
Ses racines seront desséchées par-dessous. Sa branche sera coupée en haut.
17 An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
Son souvenir disparaîtra de la terre. Il n'aura pas de nom dans la rue.
18 An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
Il sera chassé de la lumière dans les ténèbres, et chassé du monde.
19 Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
Il n'aura ni fils ni petit-fils parmi son peuple, et aucun ne reste là où il a vécu.
20 Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
Ceux qui viendront après seront étonnés de son jour, comme ceux qui les ont précédés ont été effrayés.
21 Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”
Telles sont les demeures des injustes. C'est la place de celui qui ne connaît pas Dieu. »