< Ayuba 18 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Then Bildad the Shuhite answered and said,
2 “Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
“When will you stop your talk? Consider, and afterwards we will speak.
3 Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
Why are we regarded as beasts, stupid in your sight?
4 Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
You who tear at yourself in your anger, should the earth be forsaken for you or should the rocks be removed out of their places?
5 “An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
Indeed, the light of the wicked person will be put out; the spark of his fire will not shine.
6 Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
The light will be dark in his tent; his lamp above him will be put out.
7 Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
The steps of his strength will be made short; his own plans will cast him down.
8 Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
For he will be thrown into a net by his own feet; he will walk into a pitfall.
9 Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
A trap will take him by the heel; a snare will lay hold on him.
10 An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
A noose is hidden for him on the ground; and a trap for him in the way.
11 Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
Terrors will make him afraid on every side; they will chase him at his heels.
12 Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
His wealth will turn into hunger, and calamity will be ready at his side.
13 Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
The parts of his body will be devoured; indeed, the firstborn of death will devour his parts.
14 An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
He is torn from the safety of his tent and marched off to the king of terrors.
15 Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
People not his own will live in his tent after they see that sulfur is scattered within his home.
16 Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
His roots will be dried up beneath; above will his branch be cut off.
17 An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
His memory will perish from the earth; he will have no name in the street.
18 An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
He will be driven from light into darkness and be chased out of this world.
19 Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
He will have no son or son's son among his people, nor any remaining kinfolk where he had stayed.
20 Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
Those who live in the west will be horrified at what happens to him one day; those who live in the east will be frightened by it.
21 Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”
Surely such are the homes of unrighteous people, the places of those who do not know God.”

< Ayuba 18 >