< Ayuba 18 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Then answered Bildad the Shuhite, and said,
2 “Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
How long will ye hunt for words? Consider, and afterwards we will speak.
3 Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
Wherefore are we counted as beasts, [And] are become unclean in your sight?
4 Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
Thou that tearest thyself in thine anger, Shall the earth be forsaken for thee? Or shall the rock be removed out of its place?
5 “An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
Yea, the light of the wicked shall be put out, And the spark of his fire shall not shine.
6 Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
The light shall be dark in his tent, And his lamp above him shall be put out.
7 Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
The steps of his strength shall be straitened, And his own counsel shall cast him down.
8 Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
For he is cast into a net by his own feet, And he walketh upon the toils.
9 Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
A gin shall take [him] by the heel, [And] a snare shall lay hold on him.
10 An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
A noose is hid for him in the ground, And a trap for him in the way.
11 Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
Terrors shall make him afraid on every side, And shall chase him at his heels.
12 Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
His strength shall be hunger-bitten, And calamity shall be ready at his side.
13 Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
The members of his body shall be devoured, [Yea], the first-born of death shall devour his members.
14 An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
He shall be rooted out of his tent wherein he trusteth; And he shall be brought to the king of terrors.
15 Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
There shall dwell in his tent that which is none of his: Brimstone shall be scattered upon his habitation.
16 Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
His roots shall be dried up beneath, And above shall his branch be cut off.
17 An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
His remembrance shall perish from the earth, And he shall have no name in the street.
18 An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
He shall be driven from light into darkness, And chased out of the world.
19 Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
He shall have neither son nor son’s son among his people, Nor any remaining where he sojourned.
20 Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
They that come after shall be astonished at his day, As they that went before were affrighted.
21 Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”
Surely such are the dwellings of the unrighteous, And this is the place of him that knoweth not God.

< Ayuba 18 >