< Ayuba 17 >
1 Na karaya, kwanakina sun kusa ƙarewa, kabari yana jirana.
Мій дух залама́всь, мої дні погаса́ють, — зоста́лись мені самі гроби!
2 Ba shakka masu yi mini ba’a suna kewaye da ni; idanuna suna ganin tsokanar da suke yi mini.
Дійсно, насмі́шки зо мною, й моє око в розгі́рченні їхнім ночує.
3 “Ya Allah, ka ba ni abin da ka yi mini alkawari. Wane ne zai kāre ni?
Поклади, дай заста́ву за мене Ти Сам, — хто ж то той, що умову зо мною заб'є по рука́х?
4 Ka rufe zuciyarsu yadda ba za su iya ganewa ba, saboda haka ba za ka bari su yi nasara ba.
Бо від розуміння закрив Ти їх серце тому не звели́чуєш їх.
5 In mutum ya juya wa abokansa baya don a ba shi wata lada’ya’yansa za su makance.
Він призна́чує ближніх на по́діл, а очі синів його те́мніють,
6 “Allah ya sa na zama abin da kowa yake magana a kai wanda kowa yake tofa wa miyau a fuska.
Він поставив мене за прислі́в'я в наро́дів, і став я таким, на якого плюють.
7 Idanuna ba sa gani sosai don baƙin ciki; jikina ya zama kamar inuwa kawai
З безтала́ння поте́мніло око моє, а всі члени мої — як та тінь...
8 Mutanen da suke masu adalci wannan abu ya ba su tsoro; marasa laifi sun tayar wa marasa tsoron Allah.
Праведники остовпі́ють на це, і невинний встає на безбожного.
9 Duk da haka, masu adalci za su ci gaba da tafiya a kan hanyarsu, waɗanda hannuwansu suke da tsabta kuma za su ƙara ƙarfi.
І праведний буде держа́тись дороги своєї, а хто чистору́кий — побі́льшиться в силі.
10 “Amma ku zo dukanku, ku sāke gwadawa! Ba zan sami mutum ɗaya mai hikima ba a cikinku.
Але всі ви пове́рнетеся, — і прихо́дьте, та я не зиахо́джу між вами розумного.
11 Kwanakina sun wuce, shirye-shiryena sun ɓaci haka kuma abubuwan da zuciyata take so.
Мої дні проминули, порвалися ду́ми мої, мого серця маєток, —
12 Mutanen nan sun juya rana ta zama dare. A tsakiyar duhu suka ce, ‘Haske yana kusa.’
вони мені ніч оберта́ють на день, набли́жують світло при те́мряві!
13 In kabari ne begen da nake da shi kaɗai, in na shimfiɗa gadona a cikin duhu, (Sheol )
Якщо сподіва́юсь, то тільки шео́лу, як дому свого, в темноті постелю́ своє ло́же. (Sheol )
14 In na ce wa kabari, ‘Kai ne mahaifina,’ tsutsa kuma ke ce, ‘Mahaifiyata’ ko ‘’yar’uwata,’
До гро́бу я кличу: „О батьку ти мій!“До черви́: „Моя мамо та се́стро моя!“
15 To, ina begena yake? Wane ne zai iya ganin wani bege domina?
Де ж тоді та наді́я моя? А надія моя, — хто побачить її?
16 Ko begena zai tafi tare da ni zuwa kabari ne? Ko tare za a bizne mu cikin ƙura?” (Sheol )
До шео́лових за́сувів зі́йде вона, коли зі́йдемо ра́зом до по́роху“. (Sheol )