< Ayuba 17 >

1 Na karaya, kwanakina sun kusa ƙarewa, kabari yana jirana.
Meu espírito está arruinado, meus dias vão se extinguindo, e a sepultura já etá pronta para mim.
2 Ba shakka masu yi mini ba’a suna kewaye da ni; idanuna suna ganin tsokanar da suke yi mini.
Comigo há ninguém além de zombadores, e meus olhos são obrigados a ficar diante de suas provocações.
3 “Ya Allah, ka ba ni abin da ka yi mini alkawari. Wane ne zai kāre ni?
Concede-me, por favor, uma garantia para comigo; quem [outro] há que me dê a mão?
4 Ka rufe zuciyarsu yadda ba za su iya ganewa ba, saboda haka ba za ka bari su yi nasara ba.
Pois aos corações deles tu encobriste do entendimento; portanto não os exaltarás.
5 In mutum ya juya wa abokansa baya don a ba shi wata lada’ya’yansa za su makance.
Aquele que denuncia a seus amigos em proveito próprio, também os olhos de seus filhos desfalecerão.
6 “Allah ya sa na zama abin da kowa yake magana a kai wanda kowa yake tofa wa miyau a fuska.
Ele tem me posto por ditado de povos, e em meu rosto é onde eles cospem.
7 Idanuna ba sa gani sosai don baƙin ciki; jikina ya zama kamar inuwa kawai
Por isso meus olhos se escureceram de mágoa, e todos os membros de meu corpo são como a sombra.
8 Mutanen da suke masu adalci wannan abu ya ba su tsoro; marasa laifi sun tayar wa marasa tsoron Allah.
Os íntegros pasmarão sobre isto, e o inocente se levantará contra o hipócrita.
9 Duk da haka, masu adalci za su ci gaba da tafiya a kan hanyarsu, waɗanda hannuwansu suke da tsabta kuma za su ƙara ƙarfi.
E o justo prosseguirá seu caminho, e o puro de mãos crescerá em força.
10 “Amma ku zo dukanku, ku sāke gwadawa! Ba zan sami mutum ɗaya mai hikima ba a cikinku.
Mas, na verdade, voltai-vos todos vós, e vinde agora, pois sábio nenhum acharei entre vós.
11 Kwanakina sun wuce, shirye-shiryena sun ɓaci haka kuma abubuwan da zuciyata take so.
Meus dias se passaram, meus pensamentos foram arrancados, os desejos do meu coração.
12 Mutanen nan sun juya rana ta zama dare. A tsakiyar duhu suka ce, ‘Haske yana kusa.’
Tornaram a noite em dia; a luz se encurta por causa das trevas.
13 In kabari ne begen da nake da shi kaɗai, in na shimfiɗa gadona a cikin duhu, (Sheol h7585)
Se eu esperar, o Xeol será minha casa; nas trevas estenderei minha cama. (Sheol h7585)
14 In na ce wa kabari, ‘Kai ne mahaifina,’ tsutsa kuma ke ce, ‘Mahaifiyata’ ko ‘’yar’uwata,’
À cova chamo: Tu és meu pai; e aos vermes: [Sois] minha mãe e minha irmã.
15 To, ina begena yake? Wane ne zai iya ganin wani bege domina?
Onde, pois, estaria agora minha esperança? Quanto à minha esperança, quem a poderá ver?
16 Ko begena zai tafi tare da ni zuwa kabari ne? Ko tare za a bizne mu cikin ƙura?” (Sheol h7585)
Será que ela descerá aos ferrolhos do Xeol? Descansaremos juntos no pó da terra? (Sheol h7585)

< Ayuba 17 >