< Ayuba 17 >
1 Na karaya, kwanakina sun kusa ƙarewa, kabari yana jirana.
Mon esprit s’affaiblira, mes jours seront abrégés, et il ne me reste qu’un sépulcre.
2 Ba shakka masu yi mini ba’a suna kewaye da ni; idanuna suna ganin tsokanar da suke yi mini.
Je n’ai pas péché, et mon œil vit au milieu des amertumes.
3 “Ya Allah, ka ba ni abin da ka yi mini alkawari. Wane ne zai kāre ni?
Délivrez-moi, Seigneur, et placez-moi auprès de vous; après cela, que la main de qui que ce soit combatte contre moi.
4 Ka rufe zuciyarsu yadda ba za su iya ganewa ba, saboda haka ba za ka bari su yi nasara ba.
Vous avez éloigné leur cœur de la science; c’est pourquoi ils ne seront pas exaltés.
5 In mutum ya juya wa abokansa baya don a ba shi wata lada’ya’yansa za su makance.
Il promet du butin à ses compagnons, et les yeux de ses enfants s’éteindront.
6 “Allah ya sa na zama abin da kowa yake magana a kai wanda kowa yake tofa wa miyau a fuska.
Il m’a rendu comme le brocard du peuple, et je suis un exemple devant eux.
7 Idanuna ba sa gani sosai don baƙin ciki; jikina ya zama kamar inuwa kawai
Mon œil s’est obscurci par l’indignation, et mes membres ont été réduits comme à rien.
8 Mutanen da suke masu adalci wannan abu ya ba su tsoro; marasa laifi sun tayar wa marasa tsoron Allah.
Des justes seront dans la stupeur, et un innocent sera suscité contre un hypocrite.
9 Duk da haka, masu adalci za su ci gaba da tafiya a kan hanyarsu, waɗanda hannuwansu suke da tsabta kuma za su ƙara ƙarfi.
Mais un juste garde sa voie, et celui qui a les mains pures augmentera sa force.
10 “Amma ku zo dukanku, ku sāke gwadawa! Ba zan sami mutum ɗaya mai hikima ba a cikinku.
Ainsi, vous tous, convertissez-vous; venez, et je ne trouverai parmi vous aucun sage.
11 Kwanakina sun wuce, shirye-shiryena sun ɓaci haka kuma abubuwan da zuciyata take so.
Mes jours sont passés, mes pensées se sont dissipées en tourmentant mon cœur.
12 Mutanen nan sun juya rana ta zama dare. A tsakiyar duhu suka ce, ‘Haske yana kusa.’
Elles ont changé la nuit en jour, et encore, après les ténèbres, j’espère la lumière.
13 In kabari ne begen da nake da shi kaɗai, in na shimfiɗa gadona a cikin duhu, (Sheol )
Si j’attends avec patience, l’enfer sera ma maison, et c’est dans les ténèbres que j’ai préparé mon lit. (Sheol )
14 In na ce wa kabari, ‘Kai ne mahaifina,’ tsutsa kuma ke ce, ‘Mahaifiyata’ ko ‘’yar’uwata,’
J’ai dit à la pourriture: Tu es mon père; et aux vers: Ma mère et ma sœur.
15 To, ina begena yake? Wane ne zai iya ganin wani bege domina?
Où est donc maintenant mon attente? Et ma patience, qui la considère?
16 Ko begena zai tafi tare da ni zuwa kabari ne? Ko tare za a bizne mu cikin ƙura?” (Sheol )
Tout ce qui est en moi descendra dans le plus profond de l’enfer: penses-tu qu’au moins là il y aura repos pour moi? (Sheol )