< Ayuba 17 >
1 Na karaya, kwanakina sun kusa ƙarewa, kabari yana jirana.
Mon âme est meurtrie, mes jours s’éteignent, la tombe m’attend.
2 Ba shakka masu yi mini ba’a suna kewaye da ni; idanuna suna ganin tsokanar da suke yi mini.
Ne suis-je pas en butte à des moqueries? Mes yeux ne sont-ils pas constamment témoins de leurs perfidies?
3 “Ya Allah, ka ba ni abin da ka yi mini alkawari. Wane ne zai kāre ni?
Ah! De grâce, accorde-moi ta caution! Sois toi-même mon garant vis-à-vis de toi qui voudrait s’engager pour moi?
4 Ka rufe zuciyarsu yadda ba za su iya ganewa ba, saboda haka ba za ka bari su yi nasara ba.
Car tu as fermé leur cœur à la raison; aussi ne les laisseras-tu pas triompher.
5 In mutum ya juya wa abokansa baya don a ba shi wata lada’ya’yansa za su makance.
Pour une part de butin on trahit des amis, de sorte que les yeux de leurs enfants se consument de misère.
6 “Allah ya sa na zama abin da kowa yake magana a kai wanda kowa yake tofa wa miyau a fuska.
On a fait de moi la fable des nations; je suis l’homme à qui on crache au visage.
7 Idanuna ba sa gani sosai don baƙin ciki; jikina ya zama kamar inuwa kawai
Mes yeux sont éteints par le chagrin, et tous mes organes sont comme une ombre.
8 Mutanen da suke masu adalci wannan abu ya ba su tsoro; marasa laifi sun tayar wa marasa tsoron Allah.
Les gens de bien en sont stupéfaits, et l’innocent en est révolté contre l’impie.
9 Duk da haka, masu adalci za su ci gaba da tafiya a kan hanyarsu, waɗanda hannuwansu suke da tsabta kuma za su ƙara ƙarfi.
Cependant le juste persiste dans sa conduite, et celui qui a les mains pures redouble d’énergie.
10 “Amma ku zo dukanku, ku sāke gwadawa! Ba zan sami mutum ɗaya mai hikima ba a cikinku.
Quant à vous, retournez-vous donc tous contre moi, venez! Je ne trouverai pas un sage parmi vous.
11 Kwanakina sun wuce, shirye-shiryena sun ɓaci haka kuma abubuwan da zuciyata take so.
Mes jours ont fui, mes projets sont ruinés, ces trésors de mon cœur.
12 Mutanen nan sun juya rana ta zama dare. A tsakiyar duhu suka ce, ‘Haske yana kusa.’
De la nuit ils veulent faire le jour, ils disent la lumière plus proche que les ténèbres.
13 In kabari ne begen da nake da shi kaɗai, in na shimfiɗa gadona a cikin duhu, (Sheol )
Si je n’attends plus d’autre demeure que le Cheol, si j’ai étendu ma couche dans la région des ombres; (Sheol )
14 In na ce wa kabari, ‘Kai ne mahaifina,’ tsutsa kuma ke ce, ‘Mahaifiyata’ ko ‘’yar’uwata,’
si je dis au tombeau: "Tu es mon père!" et à la vermine: "Tu es ma mère et ma sœur"
15 To, ina begena yake? Wane ne zai iya ganin wani bege domina?
où donc est mon espérance? Mon espérance, qui peut la voir?
16 Ko begena zai tafi tare da ni zuwa kabari ne? Ko tare za a bizne mu cikin ƙura?” (Sheol )
Elle a sombré jusqu’au fond du Cheol, si toutefois le repos est assuré dans la poussière. (Sheol )