< Ayuba 17 >
1 Na karaya, kwanakina sun kusa ƙarewa, kabari yana jirana.
My spirit is consumed, my days are extinct, the grave is [ready] for me.
2 Ba shakka masu yi mini ba’a suna kewaye da ni; idanuna suna ganin tsokanar da suke yi mini.
Surely there are mockers with me, and mine eye abideth in their provocation.
3 “Ya Allah, ka ba ni abin da ka yi mini alkawari. Wane ne zai kāre ni?
Give now a pledge, be surety for me with thyself; who is there that will strike hands with me?
4 Ka rufe zuciyarsu yadda ba za su iya ganewa ba, saboda haka ba za ka bari su yi nasara ba.
For thou hast hid their heart from understanding: therefore shalt thou not exalt [them].
5 In mutum ya juya wa abokansa baya don a ba shi wata lada’ya’yansa za su makance.
He that denounceth his friends for a prey, even the eyes of his children shall fail.
6 “Allah ya sa na zama abin da kowa yake magana a kai wanda kowa yake tofa wa miyau a fuska.
He hath made me also a byword of the people; and I am become an open abhorring.
7 Idanuna ba sa gani sosai don baƙin ciki; jikina ya zama kamar inuwa kawai
Mine eye also is dim by reason of sorrow, and all my members are as a shadow.
8 Mutanen da suke masu adalci wannan abu ya ba su tsoro; marasa laifi sun tayar wa marasa tsoron Allah.
Upright men shall be astonied at this, and the innocent shall stir up himself against the godless.
9 Duk da haka, masu adalci za su ci gaba da tafiya a kan hanyarsu, waɗanda hannuwansu suke da tsabta kuma za su ƙara ƙarfi.
Yet shall the righteous hold on his way, and he that hath clean hands shall wax stronger and stronger.
10 “Amma ku zo dukanku, ku sāke gwadawa! Ba zan sami mutum ɗaya mai hikima ba a cikinku.
But return ye, all of you, and come now: and I shall not find a wise man among you.
11 Kwanakina sun wuce, shirye-shiryena sun ɓaci haka kuma abubuwan da zuciyata take so.
My days are past, my purposes are broken off, even the droughts of my heart.
12 Mutanen nan sun juya rana ta zama dare. A tsakiyar duhu suka ce, ‘Haske yana kusa.’
They change the night into a day: the fight, [say they], is near unto the darkness.
13 In kabari ne begen da nake da shi kaɗai, in na shimfiɗa gadona a cikin duhu, (Sheol )
If I look for Sheol as mine house; if I have spread my couch in the darkness; (Sheol )
14 In na ce wa kabari, ‘Kai ne mahaifina,’ tsutsa kuma ke ce, ‘Mahaifiyata’ ko ‘’yar’uwata,’
If I have said to corruption, Thou art my father; to the worm, [Thou art] my mother, and my sister;
15 To, ina begena yake? Wane ne zai iya ganin wani bege domina?
Where then is my hope? and as for my hope, who shall see it?
16 Ko begena zai tafi tare da ni zuwa kabari ne? Ko tare za a bizne mu cikin ƙura?” (Sheol )
It shall go down to the bars of Sheol, when once there is rest in the dust. (Sheol )