< Ayuba 17 >

1 Na karaya, kwanakina sun kusa ƙarewa, kabari yana jirana.
My breath is corrupt, my days are extinct, the graves are ready for me.
2 Ba shakka masu yi mini ba’a suna kewaye da ni; idanuna suna ganin tsokanar da suke yi mini.
Are there not mockers with me? and does not mine eye continue in their provocation?
3 “Ya Allah, ka ba ni abin da ka yi mini alkawari. Wane ne zai kāre ni?
Lay down now, put me in a guarantor with you; who is he that will shake hands with me?
4 Ka rufe zuciyarsu yadda ba za su iya ganewa ba, saboda haka ba za ka bari su yi nasara ba.
For you have hid their heart from understanding: therefore shall you not exalt them.
5 In mutum ya juya wa abokansa baya don a ba shi wata lada’ya’yansa za su makance.
He that speaks flattery to his friends, even the eyes of his children shall fail.
6 “Allah ya sa na zama abin da kowa yake magana a kai wanda kowa yake tofa wa miyau a fuska.
He has made me also a byword of the people; and in old times I was as a timbrel.
7 Idanuna ba sa gani sosai don baƙin ciki; jikina ya zama kamar inuwa kawai
Mine eye also is dim by reason of sorrow, and all my members are as a shadow.
8 Mutanen da suke masu adalci wannan abu ya ba su tsoro; marasa laifi sun tayar wa marasa tsoron Allah.
Upright men shall be astonished at this, and the innocent shall stir up himself against the hypocrite.
9 Duk da haka, masu adalci za su ci gaba da tafiya a kan hanyarsu, waɗanda hannuwansu suke da tsabta kuma za su ƙara ƙarfi.
The righteous also shall hold on his way, and he that has clean hands shall be stronger and stronger.
10 “Amma ku zo dukanku, ku sāke gwadawa! Ba zan sami mutum ɗaya mai hikima ba a cikinku.
But as for you all, do all of you return, and come now: for I cannot find one wise man among you.
11 Kwanakina sun wuce, shirye-shiryena sun ɓaci haka kuma abubuwan da zuciyata take so.
My days are past, my purposes are broken off, even the thoughts of my heart.
12 Mutanen nan sun juya rana ta zama dare. A tsakiyar duhu suka ce, ‘Haske yana kusa.’
They change the night into day: the light is short because of darkness.
13 In kabari ne begen da nake da shi kaɗai, in na shimfiɗa gadona a cikin duhu, (Sheol h7585)
If I wait, the grave is mine house: I have made my bed in the darkness. (Sheol h7585)
14 In na ce wa kabari, ‘Kai ne mahaifina,’ tsutsa kuma ke ce, ‘Mahaifiyata’ ko ‘’yar’uwata,’
I have said to corruption, You are my father: to the worm, You are my mother, and my sister.
15 To, ina begena yake? Wane ne zai iya ganin wani bege domina?
And where is now my hope? as for my hope, who shall see it?
16 Ko begena zai tafi tare da ni zuwa kabari ne? Ko tare za a bizne mu cikin ƙura?” (Sheol h7585)
They shall go down to the bars of the pit, when our rest together is in the dust. (Sheol h7585)

< Ayuba 17 >