< Ayuba 17 >
1 Na karaya, kwanakina sun kusa ƙarewa, kabari yana jirana.
My spirit shall be wasted, my days shall be shortened, and only the grave remaineth for me.
2 Ba shakka masu yi mini ba’a suna kewaye da ni; idanuna suna ganin tsokanar da suke yi mini.
I have not sinned, and my eye abideth in bitterness.
3 “Ya Allah, ka ba ni abin da ka yi mini alkawari. Wane ne zai kāre ni?
Deliver me O Lord, and set me beside thee, and let any man’s hand fight against me.
4 Ka rufe zuciyarsu yadda ba za su iya ganewa ba, saboda haka ba za ka bari su yi nasara ba.
Thou hast set their heart far from understanding, therefore they shall not be exalted.
5 In mutum ya juya wa abokansa baya don a ba shi wata lada’ya’yansa za su makance.
He promiseth a prey to his companions, and the eyes of his children shall fail.
6 “Allah ya sa na zama abin da kowa yake magana a kai wanda kowa yake tofa wa miyau a fuska.
He hath made me as it were a byword of the people, and I am an example before them.
7 Idanuna ba sa gani sosai don baƙin ciki; jikina ya zama kamar inuwa kawai
My eye is dim through indignation, and my limbs are brought as it were to nothing.
8 Mutanen da suke masu adalci wannan abu ya ba su tsoro; marasa laifi sun tayar wa marasa tsoron Allah.
The just shall be astonished at this, and the innocent shall be raised up against the hypocrite.
9 Duk da haka, masu adalci za su ci gaba da tafiya a kan hanyarsu, waɗanda hannuwansu suke da tsabta kuma za su ƙara ƙarfi.
And the just man shall hold on his way, and he that hath clean hands shall be stronger and stronger.
10 “Amma ku zo dukanku, ku sāke gwadawa! Ba zan sami mutum ɗaya mai hikima ba a cikinku.
Wherefore be you all converted, and come, and I shall not find among you any wise man.
11 Kwanakina sun wuce, shirye-shiryena sun ɓaci haka kuma abubuwan da zuciyata take so.
My days have passed away, my thoughts are dissipated, tormenting my heart.
12 Mutanen nan sun juya rana ta zama dare. A tsakiyar duhu suka ce, ‘Haske yana kusa.’
They have turned night into day, and after darkness I hope for light again.
13 In kabari ne begen da nake da shi kaɗai, in na shimfiɗa gadona a cikin duhu, (Sheol )
If I wait hell is my house, and I have made my bed in darkness. (Sheol )
14 In na ce wa kabari, ‘Kai ne mahaifina,’ tsutsa kuma ke ce, ‘Mahaifiyata’ ko ‘’yar’uwata,’
If I have said to rottenness: Thou art my father; to worms, my mother and my sister.
15 To, ina begena yake? Wane ne zai iya ganin wani bege domina?
Where is now then my expectation, and who considereth my patience?
16 Ko begena zai tafi tare da ni zuwa kabari ne? Ko tare za a bizne mu cikin ƙura?” (Sheol )
All that I have shall go down into the deepest pit: thinkest thou that there at least I shall have rest? (Sheol )