< Ayuba 17 >

1 Na karaya, kwanakina sun kusa ƙarewa, kabari yana jirana.
I perish, carried away by the wind, and I seek for burial, and obtain [it] not.
2 Ba shakka masu yi mini ba’a suna kewaye da ni; idanuna suna ganin tsokanar da suke yi mini.
Weary I intreat; and what have I done? and strangers have stolen my goods.
3 “Ya Allah, ka ba ni abin da ka yi mini alkawari. Wane ne zai kāre ni?
Who is this? let him join hands with me.
4 Ka rufe zuciyarsu yadda ba za su iya ganewa ba, saboda haka ba za ka bari su yi nasara ba.
For thou hast hid their heart from wisdom; therefore thou shalt not exalt them.
5 In mutum ya juya wa abokansa baya don a ba shi wata lada’ya’yansa za su makance.
He shall promise mischief to [his] companions: but [their] eyes have failed for [their] children.
6 “Allah ya sa na zama abin da kowa yake magana a kai wanda kowa yake tofa wa miyau a fuska.
But thou has made me a byword amount the nations, and I am become a scorn to them.
7 Idanuna ba sa gani sosai don baƙin ciki; jikina ya zama kamar inuwa kawai
For my eyes are dimmed through pain; I have been grievously beset by all.
8 Mutanen da suke masu adalci wannan abu ya ba su tsoro; marasa laifi sun tayar wa marasa tsoron Allah.
Wonder has seized true men upon this; and let the just rise up against the transgressor.
9 Duk da haka, masu adalci za su ci gaba da tafiya a kan hanyarsu, waɗanda hannuwansu suke da tsabta kuma za su ƙara ƙarfi.
But let the faithful hold on his own way, and let him that is pure of hands take courage.
10 “Amma ku zo dukanku, ku sāke gwadawa! Ba zan sami mutum ɗaya mai hikima ba a cikinku.
Howbeit, do ye all strengthen [yourselves] and come now, for I do not find truth in you.
11 Kwanakina sun wuce, shirye-shiryena sun ɓaci haka kuma abubuwan da zuciyata take so.
My days have passed in groaning, and my heart-strings are broken.
12 Mutanen nan sun juya rana ta zama dare. A tsakiyar duhu suka ce, ‘Haske yana kusa.’
I have turned the night into day: the light is short because of darkness.
13 In kabari ne begen da nake da shi kaɗai, in na shimfiɗa gadona a cikin duhu, (Sheol h7585)
For if I remain, Hades is my habitation: and my bed has been made in darkness. (Sheol h7585)
14 In na ce wa kabari, ‘Kai ne mahaifina,’ tsutsa kuma ke ce, ‘Mahaifiyata’ ko ‘’yar’uwata,’
I have called upon death to be my father, and corruption [to be] my mother and sister.
15 To, ina begena yake? Wane ne zai iya ganin wani bege domina?
Where then is yet my hope? or [where] shall I see my good?
16 Ko begena zai tafi tare da ni zuwa kabari ne? Ko tare za a bizne mu cikin ƙura?” (Sheol h7585)
Will they go down with me to Hades, or shall we go down together to the tomb? (Sheol h7585)

< Ayuba 17 >