< Ayuba 16 >
2 “Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
Слушао сам много таквих ствари; сви сте досадни тешиоци.
3 Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
Хоће ли бити крај празним речима? Или шта те тера да тако одговараш?
4 Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
И ја бих могао говорити као ви, да сте на мом месту, гомилати на вас речи и махати главом на вас,
5 Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
Могао бих вас храбрити устима својим, и мицање усана мојих олакшало би бол ваш.
6 “Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
Ако говорим, неће одахнути бол мој; ако ли престанем, хоће ли отићи од мене?
7 Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
А сада ме је уморио; опустошио си сав збор мој.
8 Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
Навукао си на ме мрштине за сведочанство; и моја мрша подиже се на ме, и сведочи ми у очи.
9 Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
Гнев Његов растрже ме, ненавиди ме, шкргуће зубима на ме, поставши ми непријатељ сева очима својим на ме.
10 Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
Разваљују на ме уста своја, срамотно ме бију по образима, скупљају се на ме.
11 Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
Предао ме је Бог неправеднику, и у руке безбожницима бацио ме.
12 Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
Бејах миран и затре ме, и ухвативши ме за врат смрска ме и метну ме себи за белегу.
13 maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
Опколише ме Његови стрелци, цепа ми бубреге немилице, просипа на земљу жуч моју.
14 Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
Задаје ми ране на ране, и удара на ме као јунак.
15 “Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
Сашио сам кострет по кожи својој, и уваљао сам у прах славу своју.
16 Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
Лице је моје подбуло од плача, на веђама је мојим смртни сен;
17 duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
Премда нема неправде у рукама мојим, и молитва је моја чиста.
18 “Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
Земљо, не криј крв што сам пролио, и нека нема места викању мом.
19 Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
И сада ето је на небу сведок мој, сведок је мој на висини.
20 Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
Пријатељи се моји подругују мном; око моје рони сузе Богу.
21 a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
О да би се човек могао правдати с Богом, као син човечији с пријатељем својим!
22 “Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.
Јер године избројане навршују се, и полазим путем одакле се нећу вратити.