< Ayuba 16 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
respondens autem Iob dixit
2 “Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
audivi frequenter talia consolatores onerosi omnes vos estis
3 Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
numquid habebunt finem verba ventosa aut aliquid tibi molestum est si loquaris
4 Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
poteram et ego similia vestri loqui atque utinam esset anima vestra pro anima mea consolarer et ego vos sermonibus et moverem caput meum super vos
5 Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
roborarem vos ore meo et moverem labia quasi parcens vobis
6 “Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
sed quid agam si locutus fuero non quiescet dolor meus et si tacuero non recedet a me
7 Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
nunc autem oppressit me dolor meus et in nihili redacti sunt omnes artus mei
8 Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
rugae meae testimonium dicunt contra me et suscitatur falsiloquus adversus faciem meam contradicens mihi
9 Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
collegit furorem suum in me et comminans mihi infremuit contra me dentibus suis hostis meus terribilibus oculis me intuitus est
10 Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
aperuerunt super me ora sua exprobrantes percusserunt maxillam meam satiati sunt poenis meis
11 Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
conclusit me Deus apud iniquum et manibus impiorum me tradidit
12 Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
ego ille quondam opulentus repente contritus sum tenuit cervicem meam confregit me et posuit sibi quasi in signum
13 maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
circumdedit me lanceis suis convulneravit lumbos meos non pepercit et effudit in terra viscera mea
14 Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
concidit me vulnere super vulnus inruit in me quasi gigans
15 “Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
saccum consui super cutem meam et operui cinere cornu meum
16 Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
facies mea intumuit a fletu et palpebrae meae caligaverunt
17 duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
haec passus sum absque iniquitate manus meae cum haberem mundas ad Deum preces
18 “Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
terra ne operias sanguinem meum neque inveniat locum in te latendi clamor meus
19 Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
ecce enim in caelo testis meus et conscius meus in excelsis
20 Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
verbosi mei amici mei ad Deum stillat oculus meus
21 a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
atque utinam sic iudicaretur vir cum Deo quomodo iudicatur filius hominis cum collega suo
22 “Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.
ecce enim breves anni transeunt et semitam per quam non revertar ambulo

< Ayuba 16 >