< Ayuba 16 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Respondens autem Iob, dixit:
2 “Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
Audivi frequenter talia, consolatores onerosi omnes vos estis.
3 Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
Numquid habebunt finem verba ventosa? aut aliquid tibi molestum est si loquaris?
4 Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
Poteram et ego similia vestri loqui: atque utinam esset anima vestra pro anima mea: Consolarer et ego vos sermonibus, et moverem caput meum super vos:
5 Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
Roborarem vos ore meo: et moverem labia mea, quasi parcens vobis.
6 “Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
Sed quid agam? Si locutus fuero, non quiescet dolor meus: et si tacuero, non recedet a me.
7 Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
Nunc autem oppressit me dolor meus, et in nihilum redacti sunt omnes artus mei.
8 Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
Rugæ meæ testimonium dicunt contra me, et suscitatur falsiloquus adversus faciem meam contradicens mihi.
9 Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
Collegit furorem suum in me, et comminans mihi, infremuit contra me dentibus suis: hostis meus terribilibus oculis me intuitus est.
10 Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
Aperuerunt super me ora sua, et exprobrantes percusserunt maxillam meam, saciati sunt pœnis meis.
11 Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
Conclusit me Deus apud iniquum, et manibus impiorum me tradidit.
12 Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
Ego ille quondam opulentus repente contritus sum: tenuit cervicem meam, confregit me, et posuit me sibi quasi in signum.
13 maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
Circumdedit me lanceis suis, convulneravit lumbos meos, non pepercit, et effudit in terra viscera mea.
14 Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
Concidit me vulnere super vulnus, irruit in me quasi gigas.
15 “Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
Saccum consui super cutem meam, et operui cinere carnem meam.
16 Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
Facies mea intumuit a fletu, et palpebræ meæ caligaverunt.
17 duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
Hæc passus sum absque iniquitate manus meæ, cum haberem mundas ad Deum preces.
18 “Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
Terra ne operias sanguinem meum, neque inveniat in te locum latendi clamor meus.
19 Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
Ecce enim in cælo testis meus, et conscius meus in excelsis.
20 Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
Verbosi amivi mei: ad Deum stillat oculus meus.
21 a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
Atque utinam sic iudicaretur vir cum Deo, quomodo iudicatur filius hominis cum collega suo.
22 “Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.
Ecce enim breves anni transeunt, et semitam, per quam non revertar, ambulo.

< Ayuba 16 >