< Ayuba 16 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
ויען איוב ויאמר׃
2 “Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
שמעתי כאלה רבות מנחמי עמל כלכם׃
3 Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
הקץ לדברי רוח או מה ימריצך כי תענה׃
4 Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
גם אנכי ככם אדברה לו יש נפשכם תחת נפשי אחבירה עליכם במלים ואניעה עליכם במו ראשי׃
5 Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
אאמצכם במו פי וניד שפתי יחשך׃
6 “Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
אם אדברה לא יחשך כאבי ואחדלה מה מני יהלך׃
7 Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
אך עתה הלאני השמות כל עדתי׃
8 Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
ותקמטני לעד היה ויקם בי כחשי בפני יענה׃
9 Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
אפו טרף וישטמני חרק עלי בשניו צרי ילטוש עיניו לי׃
10 Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
פערו עלי בפיהם בחרפה הכו לחיי יחד עלי יתמלאון׃
11 Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
יסגירני אל אל עויל ועל ידי רשעים ירטני׃
12 Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
שלו הייתי ויפרפרני ואחז בערפי ויפצפצני ויקימני לו למטרה׃
13 maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
יסבו עלי רביו יפלח כליותי ולא יחמול ישפך לארץ מררתי׃
14 Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
יפרצני פרץ על פני פרץ ירץ עלי כגבור׃
15 “Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
שק תפרתי עלי גלדי ועללתי בעפר קרני׃
16 Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
פני חמרמרה מני בכי ועל עפעפי צלמות׃
17 duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
על לא חמס בכפי ותפלתי זכה׃
18 “Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
ארץ אל תכסי דמי ואל יהי מקום לזעקתי׃
19 Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
גם עתה הנה בשמים עדי ושהדי במרומים׃
20 Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
מליצי רעי אל אלוה דלפה עיני׃
21 a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
ויוכח לגבר עם אלוה ובן אדם לרעהו׃
22 “Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.
כי שנות מספר יאתיו וארח לא אשוב אהלך׃

< Ayuba 16 >