< Ayuba 16 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Then Job answered and said,
2 “Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
“I have heard many such things; you are all miserable comforters.
3 Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
Will useless words ever have an end? What is wrong with you that you answer like this?
4 Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
I also could speak as you do, if you were in my place; I could collect and join words together against you and shake my head at you in mockery.
5 Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
I would strengthen you with my mouth, and the quivering of my lips will bring you relief!
6 “Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
If I speak, my grief is not lessened; if I keep from speaking, how am I helped?
7 Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
But now, God, you have made me weary; you have made all my family desolate.
8 Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
You have made me dry up, which itself is a witness against me; the leanness of my body rises up against me, and it testifies against my face.
9 Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
God has torn me in his wrath and persecuted me; He grinds his teeth in rage; my enemy fastens his eyes on me as he tears me apart.
10 Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
People have gaped with open mouth at me; they have hit me reproachfully on the cheek; they have gathered together against me.
11 Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
God hands me over to ungodly people, and throws me into the hands of wicked people.
12 Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
I was at ease, and he broke me apart. Indeed, he has taken me by the neck and dashed me to pieces; he has also set me up as his target.
13 maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
His archers surround me all around; God pierces my kidneys and does not spare me; he pours out my bile on the ground.
14 Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
He smashes through my wall again and again; he runs upon me like a warrior.
15 “Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
I have sewn sackcloth on my skin; I have thrust my horn into the ground.
16 Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
My face is red with weeping; on my eyelids is the shadow of death
17 duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
although there is no violence in my hands, and my prayer is pure.
18 “Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
Earth, do not cover up my blood; let my cry have no resting place.
19 Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
Even now, see, my witness is in heaven; he who vouches for me is on high.
20 Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
My friends scoff at me, but my eye pours out tears to God.
21 a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
I ask for that witness in heaven to argue for this man with God as a man does with his neighbor!
22 “Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.
For when a few years have passed, I will go to a place from where I will not return.

< Ayuba 16 >