< Ayuba 16 >
Then responded Job, and said: —
2 “Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
I have heard many such things, Wearisome comforters, are ye all!
3 Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
Is there to be an end to windy words? Or what so strongly exciteth thee, that thou must respond?
4 Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
I also, like you, could speak, —If your soul were in the place of my soul, I could string together words against you, and could therewith shake over you my head.
5 Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
I could make you determined, by my mouth, and then my lip-solace should restrain you.
6 “Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
Though I do speak, unassuaged is my stinging pain, —And, if I forbear, of what am I relieved?
7 Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
But, now, hath he wearied me, thou hast destroyed all my family;
8 Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
And, having captured me, it hath served, as a witness; and so my wasting away hath risen up against me, in my face, it answereth.
9 Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
His anger, hath torn and persecuted me, He hath gnashed upon me with his teeth, Mine adversary, hath sharpened his eyes for me.
10 Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
They have gaped upon me with their mouth, With reproach, have they smitten my cheek, Together, against me, have they closed their ranks.
11 Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
GOD doth abandon me to him that is perverse, and, into the hands of the lawless, he throweth me headlong.
12 Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
At ease, was I when he shattered me, Yea he seized me by my neck, and dashed me in pieces, then set me up for himself as a mark:
13 maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
His archers came round against me, He clave asunder my reins, and spared not, He poured out, on the earth, my gall:
14 Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
He made a breach in me, breach upon breach, He ran upon me, like a mighty man.
15 “Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
Sackcloth, sewed I on my skin, and rolled—in the dust—my horn:
16 Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
My face, is reddened from weeping, and, upon mine eyelashes, is the death-shade: —
17 duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
Though no violence was in my hands, and, my prayer, was pure.
18 “Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
O earth! do not cover my blood, and let there be no place for mine outcry.
19 Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
Even now, lo! in the heavens, is my witness,
20 Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
And, he that voucheth for me is on high. My friends are, they who scorn me, Unto GOD, hath mine eye shed tears: —
21 a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
That one might plead, for a man, with GOD, —Even a son of man, for his friend!
22 “Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.
When, a few years, come, then, by a path by which I shall not return, shall I depart.