< Ayuba 16 >
Så tog Job til Orde og svarede:
2 “Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
"Nok har jeg hørt af sligt, besværlige Trøstere er I til Hobe!
3 Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
Får Mundsvejret aldrig Ende? Hvad ægged dig dog til at svare?
4 Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
Også jeg kunde tale som I, hvis I kun var i mit Sted, føje mine Ord imod jer og ryste på Hovedet ad jer,
5 Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
styrke jer med min Mund, ej spare på ynksomme Ord!
6 “Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
Taler jeg, mildnes min Smerte ikke og om jeg tier, hvad Lindring får jeg?
7 Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
Dog nu har han udtømt min Kraft, du bar ødelagt hele min Kreds;
8 Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
at du greb mig, gælder som Vidnesbyrd mod mig, min Magerhed vidner imod mig.
9 Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
Hans Vrede river og slider i mig, han skærer Tænder imod mig. Fjenderne hvæsser Blikket imod mig,
10 Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
de opspiler Gabet imod mig, slår mig med Hån på Kind og flokkes til Hobe omkring mig;
11 Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
Gud gav mig hen i Niddingers Vold, i gudløses Hænder kasted han mig.
12 Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
Jeg leved i Fred, så knuste han mig, han greb mig i Nakken og sønderslog mig; han stilled mig op som Skive,
13 maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
hans Pile flyver omkring mig, han borer i Nyrerne uden Skånsel, udgyder min Galde på Jorden;
14 Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
Revne på Revne slår han mig, stormer som Kriger imod mig.
15 “Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
Over min Hud har jeg syet Sæk og boret mit Horn i Støvel;
16 Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
mit Ansigt er rødt af Gråd, mine Øjenlåg hyllet i Mørke,
17 duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
skønt der ikke er Vold i min Hånd, og skønt min Bøn er ren!
18 “Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
Dølg ikke, Jord, mit Blod, mit Skrig komme ikke til Hvile!
19 Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
Alt nu er mit Vidne i Himlen, min Talsmand er i det høje;
20 Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
gid min Ven lod sig finde! Mit Øje vender sig med Tårer til Gud,
21 a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
at han skifter Ret mellem Manden og Gud, mellem Mennesket og hans Ven!
22 “Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.
Thi talte er de kommende År, jeg skal ud på en Færd, jeg ej vender hjem fra.