< Ayuba 16 >
2 “Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
Slyšel jsem již podobných věcí mnoho; všickni vy nepříjemní jste těšitelé.
3 Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
Bude-liž kdy konec slovům povětrným? Aneb co tě popouzí, že tak mluvíš?
4 Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
Zdaliž bych já tak mluviti mohl, jako vy, kdybyste byli na místě mém? Shromažďoval-li bych proti vám slova, aneb potřásal na vás hlavou svou?
5 Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
Nýbrž posiloval bych vás ústy svými, a otvírání rtů mých krotilo by bolest.
6 “Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
Buď že mluvím, neumenšuje se bolesti mé, buď že tak nechám, neodchází ode mne.
7 Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
Ale ustavičně zemdlívá mne; nebo jsi mne, ó Bože, zbavil všeho shromáždění mého.
8 Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
A vrásky jsi mi zdělal; což mám za svědka, ano patrná na mně hubenost má na tváři mé to osvědčuje.
9 Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
Prchlivost jeho zachvátila mne, a vzal mne v nenávist, škřipě na mne zuby svými; jako nepřítel můj zaostřil oči své na mne.
10 Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
Rozedřeli na mne ústa svá, potupně mne poličkujíce, proti mně se shromáždivše.
11 Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
Vydal mne Bůh silný nešlechetníku, a v ruce bezbožných uvedl mne.
12 Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
Pokoje jsem užíval, však potřel mne, a uchopiv mne za šíji mou, roztříštil mne, a vystavil mne sobě za cíl.
13 maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
Obklíčili mne střelci jeho, rozťal ledví má beze vší lítosti, a vylil na zem žluč mou.
14 Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
Ranil mne ranou na ránu, outok učinil na mne jako silný.
15 “Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
Žíni jsem ušil na zjízvenou kůži svou, a zohavil jsem v prachu sílu svou.
16 Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
Tvář má oduřavěla od pláče, a na víčkách mých stín smrti jest.
17 duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
Ne pro nějaké bezpraví v rukou mých; nebo i modlitba má čistá jest.
18 “Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
Ó země, nepřikrývej krve mé, a nechť nemá místa volání mé.
19 Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
Aj, nyní jestiť i v nebesích svědek můj, svědek můj, pravím, jest na výsostech.
20 Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
Ó mudráci moji, přátelé moji, k Bohuť slzí oko mé.
21 a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
Ó by lze bylo muži v hádku s ním se vydati, jako synu člověka s přítelem svým.
22 “Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.
Nebo léta mně odečtená přicházejí, a cestou, kterouž se zase nenavrátím, již se beru.