< Ayuba 16 >
2 “Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
像這樣的話,我聽了許多;你們的安慰反使人煩惱。
3 Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
這些風涼話何時了﹖或者有什麼事迫你非說不可﹖
4 Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
若是你們處在我的境遇中,我也會說像你們所說的話,也會花言巧語譏笑你們,向你們搖頭。
5 Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
我也會以口舌寬慰你們,搖唇鼓舌來減輕你們的痛苦。
6 “Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
我若講話,痛苦並不停止;我若閉口不言,難道痛苦就離開我﹖
7 Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
現今天主的確叫我厭倦,使我每個親人都遠離了我;
8 Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
使我憔悴,以指證我;使我消瘦,當面非難我。
9 Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
他在憤怒中撕裂我,窘迫我,向我咬牙切齒;我仇人鋒利的眼睛常盯著我。
10 Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
他們張開大口想吞噬我,責罵著打我的面頰,一起擁上前來攻擊我。
11 Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
天主將我交於不義之人,將我丟在惡人手中。
12 Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
我原來安寧,他卻折磨我,抓住我的脖子,粉碎我,又拿我當作他的箭靶。
13 maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
他的箭矢四面射擊我,射穿我的腰,毫不留情,使我的膽傾流於地。
14 Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
他將我撕裂粉碎,有如武士向我跑來。
15 “Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
我縫麻衣包裹我的皮膚,使我額角插入塵土。
16 Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
我的臉因哭泣發紅,我睫眉間滿是暗影;
17 duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
我的手雖沒有行過殘暴的事,而我的祈禱,又往往純正。
18 “Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
地啊! 不要掩蓋我的血。願我的呼聲無休息的餘地!
19 Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
看啊! 連現今在天上有我的見證,在高處有我的中保。
20 Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
我的哀號上徹於天,在天主前我的雙目流淚不止。
21 a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
惟願人與天主之間有一中人,猶如人與人之間一樣!
22 “Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.
因為我的年數將盡,快要走上那條一去不返的路途。