< Ayuba 15 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Kisha Elifazi Mtemani akajibu:
2 “Mutum mai hikima zai amsa da surutai marasa kan gado ko yă cika cikinsa da iskar gabas?
“Je, mtu mwenye hekima hujibu kwa mawazo matupu, au kujaza tumbo lake kwa upepo wenye joto wa mashariki?
3 Ko zai yi gardama da maganganun wofi maganganu marasa amfani?
Je, aweza kubishana juu ya maneno yasiyofaa, kwa hotuba zisizo na maana?
4 Amma ka ma rena Allah ka hana a yi addu’a gare shi.
Lakini unadhoofisha hata uchaji wa Mungu na kuzuia ibada mbele za Mungu.
5 Zunubanka ne suke gaya maka abin da za ka ce; kana magana kamar mai wayo.
Dhambi yako inasukuma kinywa chako, nawe umechagua ulimi wa hila.
6 Bakinka zai kai ka yă baro, ba nawa ba; maganar bakinka za tă juya a kanka.
Kinywa chako mwenyewe kinakuhukumu, wala si changu; midomo yako mwenyewe inashuhudia dhidi yako.
7 “Kai ne mutum na farko da aka fara haihuwa? Ko kai ne aka fara halitta kafin tuddai?
“Je, wewe ni mtu wa kwanza kuzaliwa? Ulizaliwa kabla ya vilima?
8 Kana sauraron shawarar Allah? Ko kana gani kai kaɗai ne mai hikima?
Je, wewe husikiliza mashauri ya siri ya Mungu? Je, wewe unaizuia hekima iwe yako mwenyewe?
9 Me ka sani da ba mu sani ba? Wane fahimi kake da shi da ba mu da shi?
Wewe unajua kitu gani tusichokijua sisi? Unafahamu kitu gani tusichokifahamu sisi?
10 Masu furfura da tsofaffi suna gefenmu mutanen da sun girme babanka.
Wale wenye mvi na wazee wako upande wetu, watu ambao ni wazee hata kuliko baba yako.
11 Ta’aziyyar Allah ba tă ishe ka ba. Maganarsa mai laushi ba tă ishe ka ba?
Je, faraja za Mungu hazikutoshi, au maneno yaliyosemwa kwako kwa upole si kitu?
12 Don me ka bar zuciyarka ta kwashe ka, kuma don me idanunka suke haske,
Kwa nini moyo wako unakudanganya, na kwa nini macho yako yanangʼaa,
13 har kake fushi da Allah kake kuma faɗar waɗannan maganganu daga bakinka?
ili kwamba upate kutoa hasira yako dhidi ya Mungu, na kumwaga maneno kama hayo kutoka kinywani mwako?
14 “Mene ne mutum, har da zai zama da tsarki, ko kuma mace ta haife shi, har yă iya zama mai adalci?
“Mwanadamu ni kitu gani, hata aweze kuwa safi, au yeye aliyezaliwa na mwanamke, hata aweze kuwa mwadilifu?
15 In Allah bai nuna amincewa ga tsarkakansa ba, in har sammai ba su da tsarki a idonsa,
Kama Mungu hawaamini watakatifu wake, kama hata mbingu zenyewe si safi machoni pake,
16 mutum fa, wanda yake da mugunta da lalacewa, wanda yake shan mugunta kamar ruwa!
sembuse mwanadamu ambaye ni mwovu na mpotovu, ambaye hunywa uovu kama anywavyo maji!
17 “Ka saurare ni, zan kuma yi maka bayani; bari in gaya maka abin da na gani,
“Nisikilize mimi nami nitakueleza, acha nikuambie yale niliyoyaona,
18 abin da masu hikima suka ce, ba tare da sun ɓoye wani abu da suka samu daga wurin iyayensu ba
ambayo watu wenye hekima wameyanena, bila kuficha lolote walilopokea toka kwa baba zao
19 (waɗanda su ne masu ƙasar kafin baƙi su shigo ƙasar).
(wakati ambao wao peke yao ndio walipewa nchi, hakuna mgeni aliyepita miongoni mwao):
20 Dukan kwanakin ransa mugu yana shan wahala, wahala kaɗai zai yi ta sha.
Mtu mwovu siku zake zote hupata mateso, miaka yote aliwekewa mkorofi.
21 Ƙara mai bantsoro za tă cika kunnuwansa’yan fashi za su kai masa hari.
Sauti za kutisha hujaa masikioni mwake; katika kufanikiwa kwake, wanyangʼanyi humshambulia.
22 Yana jin tsoron duhu domin za a kashe shi da takobi.
Hukata tamaa kuokoka gizani; amewekwa kwa ajili ya upanga.
23 Yana ta yawo, abinci don ungulaye; ya san ranar duhu tana kusa.
Hutangatanga, akitafuta chakula; anajua kwamba siku ya giza iko karibu.
24 Ɓacin rai da baƙin ciki sun cika shi, kamar sarkin da yake shirin yaƙi,
Taabu na maumivu makuu vinamtia hofu; humshinda kama mfalme aliye tayari kwa vita,
25 domin ya nuna wa Allah yatsa ya rena Allah Maɗaukaki,
kwa sababu amemkunjia Mungu ngumi yake na kujigamba dhidi ya Mwenyezi,
26 ya tasar masa da faɗa da garkuwa mai kauri da kuma ƙarfi.
kwa kiburi akishambulia dhidi ya Mungu akiwa na ngao nene, iliyo imara.
27 “Ko da yake fuskarsa ta cika da kumatu kuma yana da tsoka ko’ina,
“Ingawa uso wake umefunikwa na mafuta kwa unene na kiuno chake kimevimba kwa kunenepa,
28 zai yi gādon garuruwan da suka lalace, da kuma gidajen da ba wanda yake zama a ciki, gidajen da sun zama tarkace.
ataishi katika miji ya magofu, na katika nyumba ambazo haziishi mwanadamu yeyote, nyumba zinazokuwa vifusi.
29 Ba zai sāke zama mai arziki ba, dukiyarsa ba za tă dawwama ba, abin da ya mallaka kuma ba zai bazu a ƙasar ba.
Hatatajirika tena, nao utajiri wake hautadumu, wala mali zake hazitakuwa nyingi juu ya nchi.
30 Ba zai tsere wa duhu ba; wuta za tă ƙona rassansa, kuma numfashi daga bakin Allah zai hallaka shi.
Hatatoka gizani; mwali wa moto utanyausha machipukizi yake, nayo pumzi ya kinywa cha Mungu itamwondolea mbali.
31 Kada yă ruɗi kansa ta wurin dogara ga abin da ba shi da amfani domin ba zai samu wani abu ba daga ciki.
Asijidanganye mwenyewe kutumainia ubatili, kwa kuwa hatapata malipo yoyote.
32 Kafin lokacinsa yă cika, za a gama biyansa duka, kuma rassansa ba za su ba da amfani ba.
Atakuwa amelipwa kikamilifu kabla ya wakati wake, nayo matawi yake hayatastawi.
33 Zai zama kamar itacen inabi wanda’ya’yansa suka kakkaɓe kafin su nuna, kamar itacen zaitun zai zubar da furensa.
Atafanana na mzabibu uliopukutishwa matunda yake kabla hayajaiva, kama mzeituni unaodondosha maua yake.
34 Gama marasa tsoron Allah za su zama marasa ba da’ya’ya, wuta kuma za tă ƙona tenti na masu son cin hanci.
Kwa kuwa jamii ya wasiomcha Mungu watakuwa tasa, nao moto utateketeza hema za wale wanaopenda rushwa.
35 Suna yin cikin rikici su kuma haifi mugunta; cikinsu yana cike da ruɗami.”
Hutunga mimba ya madhara na kuzaa uovu; matumbo yao huumba udanganyifu.”

< Ayuba 15 >