< Ayuba 15 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Då tok Elifaz frå Teman til ords og sagde:
2 “Mutum mai hikima zai amsa da surutai marasa kan gado ko yă cika cikinsa da iskar gabas?
«Kjem svar i vind og ver frå vismann? Fyller han barmen sin med storm?
3 Ko zai yi gardama da maganganun wofi maganganu marasa amfani?
Vil han med ugangstale lasta? Med ord som nyttelause er?
4 Amma ka ma rena Allah ka hana a yi addu’a gare shi.
Otten for Gud den bryt du ned og skjeplar andakt for Guds åsyn.
5 Zunubanka ne suke gaya maka abin da za ka ce; kana magana kamar mai wayo.
For syndi styrer munnen din; du talar som dei falske talar.
6 Bakinka zai kai ka yă baro, ba nawa ba; maganar bakinka za tă juya a kanka.
Din munn deg dømer, ikkje eg; og dine lippor vitnar mot deg.
7 “Kai ne mutum na farko da aka fara haihuwa? Ko kai ne aka fara halitta kafin tuddai?
Vart fyrst av menneskje du fødd? Vert fyre haugarne du avla?
8 Kana sauraron shawarar Allah? Ko kana gani kai kaɗai ne mai hikima?
Var du i Guds rådleggjing med? Og fekk du visdom til deg rana?
9 Me ka sani da ba mu sani ba? Wane fahimi kake da shi da ba mu da shi?
Kva veit du som me ikkje veit? Kva skynar du som me ei kjenner?
10 Masu furfura da tsofaffi suna gefenmu mutanen da sun girme babanka.
Gråhærd og gamling er hjå oss; han eldre er enn jamvel far din.
11 Ta’aziyyar Allah ba tă ishe ka ba. Maganarsa mai laushi ba tă ishe ka ba?
Er trøyst frå Gud det altfor ring? Vanvyrder du eit rolegt ord?
12 Don me ka bar zuciyarka ta kwashe ka, kuma don me idanunka suke haske,
Kvi let du hugen eggja deg? Kvi let du auga rulla vilt?
13 har kake fushi da Allah kake kuma faɗar waɗannan maganganu daga bakinka?
For imot Gud din harm du snur og let or munnen ordi strøyma.
14 “Mene ne mutum, har da zai zama da tsarki, ko kuma mace ta haife shi, har yă iya zama mai adalci?
Kor kann vel mannen vera rein? Og kvinnefødde hava rett?
15 In Allah bai nuna amincewa ga tsarkakansa ba, in har sammai ba su da tsarki a idonsa,
På sine heilage han lit ei; for honom er’kje himmeln rein,
16 mutum fa, wanda yake da mugunta da lalacewa, wanda yake shan mugunta kamar ruwa!
langt mindre då ein styggeting, ein mann som urett drikk som med vatn.
17 “Ka saurare ni, zan kuma yi maka bayani; bari in gaya maka abin da na gani,
Eg vil deg læra; høyr på meg! Det som eg såg, vil eg deg melda,
18 abin da masu hikima suka ce, ba tare da sun ɓoye wani abu da suka samu daga wurin iyayensu ba
det som vismenner segja kann, og ei hev dult frå sine feder,
19 (waɗanda su ne masu ƙasar kafin baƙi su shigo ƙasar).
dei som åleine landet åtte, og ingen framand kom bland deim.
20 Dukan kwanakin ransa mugu yana shan wahala, wahala kaɗai zai yi ta sha.
Den vonde stødt i uro liver, for valdsmann gøymt er fåe år.
21 Ƙara mai bantsoro za tă cika kunnuwansa’yan fashi za su kai masa hari.
I øyro rædsletonar ljomar; fyrr han veit av, kjem tynaren.
22 Yana jin tsoron duhu domin za a kashe shi da takobi.
Han trur’kje han kann fly frå myrkret; han venta lyt det kvasse sverd.
23 Yana ta yawo, abinci don ungulaye; ya san ranar duhu tana kusa.
Han leitar etter brød: Kvar er det? Han veit, ein myrk dag er for hand.
24 Ɓacin rai da baƙin ciki sun cika shi, kamar sarkin da yake shirin yaƙi,
Naud, trengsla skræmer, tyngjer honom, liksom ein konge budd til strid.
25 domin ya nuna wa Allah yatsa ya rena Allah Maɗaukaki,
For imot Gud han lyfte handi og våga tråssa Allvalds-Gud,
26 ya tasar masa da faɗa da garkuwa mai kauri da kuma ƙarfi.
han storma fram med nakken lyft, med vern utav skjold-ryggjer sterke;
27 “Ko da yake fuskarsa ta cika da kumatu kuma yana da tsoka ko’ina,
han dekte andlitet med feitt og gjorde sine lender feite.
28 zai yi gādon garuruwan da suka lalace, da kuma gidajen da ba wanda yake zama a ciki, gidajen da sun zama tarkace.
Han budde i bannstøytte byar, i hus som ingen burde bu i, men til grushaugar etla var.
29 Ba zai sāke zama mai arziki ba, dukiyarsa ba za tă dawwama ba, abin da ya mallaka kuma ba zai bazu a ƙasar ba.
Han vart’kje rik, hans gods kverv burt, hans grøda luter ei mot jordi.
30 Ba zai tsere wa duhu ba; wuta za tă ƙona rassansa, kuma numfashi daga bakin Allah zai hallaka shi.
Han kann’kje koma undan myrkret. Hans greiner turkast burt i hiten, og han kjem burt ved hans munns ande.
31 Kada yă ruɗi kansa ta wurin dogara ga abin da ba shi da amfani domin ba zai samu wani abu ba daga ciki.
Trur han på fåfengd, vert han narra, og berre fåfengd haustar han.
32 Kafin lokacinsa yă cika, za a gama biyansa duka, kuma rassansa ba za su ba da amfani ba.
Fyrr dagen kjem, då vert det uppfyllt, hans palmegreiner grønkar ikkje.
33 Zai zama kamar itacen inabi wanda’ya’yansa suka kakkaɓe kafin su nuna, kamar itacen zaitun zai zubar da furensa.
Lik vinstokk misser han si druva, spiller sin blom som oljetreet.
34 Gama marasa tsoron Allah za su zama marasa ba da’ya’ya, wuta kuma za tă ƙona tenti na masu son cin hanci.
Ein syndarflokk set ingi frukt, og elden øyder mute- tjeldi.
35 Suna yin cikin rikici su kuma haifi mugunta; cikinsu yana cike da ruɗami.”
Dei avlar møda, føder tjon, og svik i fanget sitt dei nører.»

< Ayuba 15 >