< Ayuba 15 >
1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
そこでテマンびとエリパズは答えて言った、
2 “Mutum mai hikima zai amsa da surutai marasa kan gado ko yă cika cikinsa da iskar gabas?
「知者はむなしき知識をもって答えるであろうか。東風をもってその腹を満たすであろうか。
3 Ko zai yi gardama da maganganun wofi maganganu marasa amfani?
役に立たない談話をもって論じるであろうか。無益な言葉をもって争うであろうか。
4 Amma ka ma rena Allah ka hana a yi addu’a gare shi.
ところがあなたは神を恐れることを捨て、神の前に祈る事をやめている。
5 Zunubanka ne suke gaya maka abin da za ka ce; kana magana kamar mai wayo.
あなたの罪はあなたの口を教え、あなたは悪賢い人の舌を選び用いる。
6 Bakinka zai kai ka yă baro, ba nawa ba; maganar bakinka za tă juya a kanka.
あなたの口みずからあなたの罪を定める、わたしではない。あなたのくちびるがあなたに逆らって証明する。
7 “Kai ne mutum na farko da aka fara haihuwa? Ko kai ne aka fara halitta kafin tuddai?
あなたは最初に生れた人であるのか。山よりも先に生れたのか。
8 Kana sauraron shawarar Allah? Ko kana gani kai kaɗai ne mai hikima?
あなたは神の会議にあずかったのか。あなたは知恵を独占しているのか。
9 Me ka sani da ba mu sani ba? Wane fahimi kake da shi da ba mu da shi?
あなたが知るものはわれわれも知るではないか。あなたが悟るものはわれわれも悟るではないか。
10 Masu furfura da tsofaffi suna gefenmu mutanen da sun girme babanka.
われわれの中にはしらがの人も、年老いた人もあって、あなたの父よりも年上だ。
11 Ta’aziyyar Allah ba tă ishe ka ba. Maganarsa mai laushi ba tă ishe ka ba?
神の慰めおよびあなたに対するやさしい言葉も、あなたにとって、あまりに小さいというのか。
12 Don me ka bar zuciyarka ta kwashe ka, kuma don me idanunka suke haske,
どうしてあなたの心は狂うのか。どうしてあなたの目はしばたたくのか。
13 har kake fushi da Allah kake kuma faɗar waɗannan maganganu daga bakinka?
あなたが神にむかって気をいらだて、このような言葉をあなたの口から出すのはなぜか。
14 “Mene ne mutum, har da zai zama da tsarki, ko kuma mace ta haife shi, har yă iya zama mai adalci?
人はいかなる者か、どうしてこれは清くありえよう。女から生れた者は、どうして正しくありえよう。
15 In Allah bai nuna amincewa ga tsarkakansa ba, in har sammai ba su da tsarki a idonsa,
見よ、神はその聖なる者にすら信を置かれない、もろもろの天も彼の目には清くない。
16 mutum fa, wanda yake da mugunta da lalacewa, wanda yake shan mugunta kamar ruwa!
まして憎むべき汚れた者、また不義を水のように飲む人においては。
17 “Ka saurare ni, zan kuma yi maka bayani; bari in gaya maka abin da na gani,
わたしはあなたに語ろう、聞くがよい。わたしは自分の見た事を述べよう。
18 abin da masu hikima suka ce, ba tare da sun ɓoye wani abu da suka samu daga wurin iyayensu ba
これは知者たちがその先祖からうけて、隠す所なく語り伝えたものである。
19 (waɗanda su ne masu ƙasar kafin baƙi su shigo ƙasar).
彼らにのみこの地は授けられて、他国人はその中に行き来したことがなかった。
20 Dukan kwanakin ransa mugu yana shan wahala, wahala kaɗai zai yi ta sha.
悪しき人は一生の間、もだえ苦しむ。残酷な人には年の数が定められている。
21 Ƙara mai bantsoro za tă cika kunnuwansa’yan fashi za su kai masa hari.
その耳には恐ろしい音が聞え、繁栄の時にも滅ぼす者が彼に臨む。
22 Yana jin tsoron duhu domin za a kashe shi da takobi.
彼は、暗やみから帰りうるとは信ぜず、つるぎにねらわれる。
23 Yana ta yawo, abinci don ungulaye; ya san ranar duhu tana kusa.
彼は食物はどこにあるかと言いつつさまよい、暗き日が手近に備えられてあるのを知る。
24 Ɓacin rai da baƙin ciki sun cika shi, kamar sarkin da yake shirin yaƙi,
悩みと苦しみとが彼を恐れさせ、戦いの備えをした王のように彼に打ち勝つ。
25 domin ya nuna wa Allah yatsa ya rena Allah Maɗaukaki,
これは彼が神に逆らってその手を伸べ、全能者に逆らって高慢にふるまい、
26 ya tasar masa da faɗa da garkuwa mai kauri da kuma ƙarfi.
盾の厚い面をもって強情に、彼にはせ向かうからだ。
27 “Ko da yake fuskarsa ta cika da kumatu kuma yana da tsoka ko’ina,
また彼は脂肪をもってその顔をおおい、その腰には脂肪の肉を集め、
28 zai yi gādon garuruwan da suka lalace, da kuma gidajen da ba wanda yake zama a ciki, gidajen da sun zama tarkace.
滅ぼされた町々に住み、人の住まない家、荒塚となる所におるからだ。
29 Ba zai sāke zama mai arziki ba, dukiyarsa ba za tă dawwama ba, abin da ya mallaka kuma ba zai bazu a ƙasar ba.
彼は富める者とならず、その富はながく続かない、また地に根を張ることはない。
30 Ba zai tsere wa duhu ba; wuta za tă ƙona rassansa, kuma numfashi daga bakin Allah zai hallaka shi.
彼は暗やみからのがれることができない。炎はその若枝を枯らし、その花は風に吹き去られる。
31 Kada yă ruɗi kansa ta wurin dogara ga abin da ba shi da amfani domin ba zai samu wani abu ba daga ciki.
彼をしてみずから欺いて、むなしい事にたよらせてはならない。その報いはむなしいからだ。
32 Kafin lokacinsa yă cika, za a gama biyansa duka, kuma rassansa ba za su ba da amfani ba.
彼の時のこない前にその事がなし遂げられ、彼の枝は緑とならないであろう。
33 Zai zama kamar itacen inabi wanda’ya’yansa suka kakkaɓe kafin su nuna, kamar itacen zaitun zai zubar da furensa.
彼はぶどうの木のように、その熟さない実をふり落すであろう。またオリブの木のように、その花を落すであろう。
34 Gama marasa tsoron Allah za su zama marasa ba da’ya’ya, wuta kuma za tă ƙona tenti na masu son cin hanci.
神を信じない者のやからは子なく、まいないによる天幕は火で焼き滅ぼされるからだ。
35 Suna yin cikin rikici su kuma haifi mugunta; cikinsu yana cike da ruɗami.”
彼らは害悪をはらみ、不義を生み、その腹は偽りをつくる」。