< Ayuba 15 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Darauf erwidert Eliphaz von Teman also:
2 “Mutum mai hikima zai amsa da surutai marasa kan gado ko yă cika cikinsa da iskar gabas?
"Kann denn ein Weiser so unsinnige Beweise bringen und sich in solcher Hohlheit blähen?
3 Ko zai yi gardama da maganganun wofi maganganu marasa amfani?
Kann er Beweis mit Reden führen, die nichts taugen, mit Sprüchen, die nichts nütze sind?
4 Amma ka ma rena Allah ka hana a yi addu’a gare shi.
Du machst die Gottesfurcht zunichte, zerstörst die Andacht vor der Gottheit,
5 Zunubanka ne suke gaya maka abin da za ka ce; kana magana kamar mai wayo.
wenn deine Schuld dich lehrt, also zu reden, und du Verschmitzter Redeweise wählst.
6 Bakinka zai kai ka yă baro, ba nawa ba; maganar bakinka za tă juya a kanka.
Dein eigener Mund verdammt dich und nicht ich; die eigenen Lippen strafen dich.
7 “Kai ne mutum na farko da aka fara haihuwa? Ko kai ne aka fara halitta kafin tuddai?
Warst du als Erstlingsmensch geboren und kamst du vor den Hügeln auf die Welt,
8 Kana sauraron shawarar Allah? Ko kana gani kai kaɗai ne mai hikima?
und hörtest du im Rate Gottes zu und holtest Weisheit dir allein?
9 Me ka sani da ba mu sani ba? Wane fahimi kake da shi da ba mu da shi?
Was weißt du, und wir wüßten's nicht, verstehst, was unbekannt uns wäre?
10 Masu furfura da tsofaffi suna gefenmu mutanen da sun girme babanka.
Sind unter uns doch graue Häupter, mehr als betagt genug, um Vater dir zu sein.
11 Ta’aziyyar Allah ba tă ishe ka ba. Maganarsa mai laushi ba tă ishe ka ba?
Ist dir die Gotteströstung zu gering, das Wort, das sanft an dich ergeht?
12 Don me ka bar zuciyarka ta kwashe ka, kuma don me idanunka suke haske,
Warum reißt dich ein Unmut fort? Was blicken deine Augen finster,
13 har kake fushi da Allah kake kuma faɗar waɗannan maganganu daga bakinka?
daß deinen Geist du Gott zurückzugeben trachtest? Nur mit dem Munde freilich hast du das gesagt.
14 “Mene ne mutum, har da zai zama da tsarki, ko kuma mace ta haife shi, har yă iya zama mai adalci?
Was ist der Mensch, daß rein er wäre, gerecht der Weibgeborene?
15 In Allah bai nuna amincewa ga tsarkakansa ba, in har sammai ba su da tsarki a idonsa,
Selbst seinen Heiligen traut er nicht; der Himmel ist nicht rein in seinen Augen,
16 mutum fa, wanda yake da mugunta da lalacewa, wanda yake shan mugunta kamar ruwa!
geschweige der Abscheuliche, Verdorbene, der Mensch, der Sünde wie das Wasser trinkt.
17 “Ka saurare ni, zan kuma yi maka bayani; bari in gaya maka abin da na gani,
Ich will dich lehren; hör mir zu. Was ich geschaut, will ich dir sagen,
18 abin da masu hikima suka ce, ba tare da sun ɓoye wani abu da suka samu daga wurin iyayensu ba
was Weise einst verkündet, was ihre Väter ihnen nicht verhehlt,
19 (waɗanda su ne masu ƙasar kafin baƙi su shigo ƙasar).
die noch allein im Lande saßen, zu denen noch kein Fremder kam.
20 Dukan kwanakin ransa mugu yana shan wahala, wahala kaɗai zai yi ta sha.
Des Bösen Leben ist voll Angst; nur wenig Jahre sind für den Gewaltmenschen bestimmt.
21 Ƙara mai bantsoro za tă cika kunnuwansa’yan fashi za su kai masa hari.
Der Schrecken hallt in seinem Ohr; wiewohl in Sicherheit, wird er vom Räuber überfallen schon.
22 Yana jin tsoron duhu domin za a kashe shi da takobi.
Er gibt den Glauben auf, dem Dunkel zu entrinnen; er ist bestimmt für blutigen Tod
23 Yana ta yawo, abinci don ungulaye; ya san ranar duhu tana kusa.
und wird ein Fraß der Geier. Er weiß, ihm ist ein finsterer Tag von ihm bestimmt.
24 Ɓacin rai da baƙin ciki sun cika shi, kamar sarkin da yake shirin yaƙi,
Ihn schreckt die Not; ihn überfällt die Drangsalszeit gleich einem kampfbereiten Hahn.
25 domin ya nuna wa Allah yatsa ya rena Allah Maɗaukaki,
Weil gegen Gott die Hand er ausgestreckt und dem Allmächtigen er Trotz geboten,
26 ya tasar masa da faɗa da garkuwa mai kauri da kuma ƙarfi.
so stürmt er gegen ihn, mit seines rauhen Schildes Wölbung.
27 “Ko da yake fuskarsa ta cika da kumatu kuma yana da tsoka ko’ina,
Er deckt mit dem Visier sein Angesicht, legt einen Panzerschurz um seine Lenden.
28 zai yi gādon garuruwan da suka lalace, da kuma gidajen da ba wanda yake zama a ciki, gidajen da sun zama tarkace.
Nur in verfemten Städten noch kann jener siedeln, in unbewohnbaren Gebäuden, die schon dem Abbruch sind verfallen.
29 Ba zai sāke zama mai arziki ba, dukiyarsa ba za tă dawwama ba, abin da ya mallaka kuma ba zai bazu a ƙasar ba.
Er wird nicht wieder reich, noch hat Bestand je seine Habe; er schlägt im Boden nimmer Wurzel.
30 Ba zai tsere wa duhu ba; wuta za tă ƙona rassansa, kuma numfashi daga bakin Allah zai hallaka shi.
Der Finsternis entgeht er nicht, es dörrt die Hitze seine Zweige, und seine Blüten fallen durch den Sturmwind ab.
31 Kada yă ruɗi kansa ta wurin dogara ga abin da ba shi da amfani domin ba zai samu wani abu ba daga ciki.
Zu denen, die auf Nichtiges vertrauen, irrt er hin; sein Entgelt ist das Nichts.
32 Kafin lokacinsa yă cika, za a gama biyansa duka, kuma rassansa ba za su ba da amfani ba.
Noch vor der Zeit verwelken sie, und seine Zweige grünen nimmer.
33 Zai zama kamar itacen inabi wanda’ya’yansa suka kakkaɓe kafin su nuna, kamar itacen zaitun zai zubar da furensa.
Er wirft gleich einem Weinstock seine Früchte ab, wirft wie der Ölbaum seine Blüte hin.
34 Gama marasa tsoron Allah za su zama marasa ba da’ya’ya, wuta kuma za tă ƙona tenti na masu son cin hanci.
Des Frevlers Rotte ist ja unfruchtbar, und Feuer frißt des Unrechts Zelte.
35 Suna yin cikin rikici su kuma haifi mugunta; cikinsu yana cike da ruɗami.”
Sie brüten Unheil, hecken Ungemach, und ihres Leibes Frucht ist Trug."

< Ayuba 15 >