< Ayuba 14 >
1 “Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
EL HOMBRE nacido de mujer, corto de días, y harto de sinsabores:
2 Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
Que sale como una flor y es cortado; y huye como la sombra, y no permanece.
3 Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
¿Y sobre éste abres tus ojos, y me traes á juicio contigo?
4 Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
¿Quién hará limpio de inmundo? Nadie.
5 An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
Ciertamente sus días están determinados, y el número de sus meses está cerca de ti: tú le pusiste términos, de los cuales no pasará.
6 Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
Si tú lo dejares, él dejará [de ser]: entre tanto deseará, como el jornalero, su día.
7 “Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
Porque si el árbol fuere cortado, aun queda de él esperanza; retoñecerá aún, y sus renuevos no faltarán.
8 Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
Si se envejeciere en la tierra su raíz, y su tronco fuere muerto en el polvo,
9 Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
Al percibir el agua reverdecerá, y hará copa como planta.
10 Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
Mas el hombre morirá, y será cortado; y perecerá el hombre, ¿y dónde estará él?
11 Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
Las aguas de la mar se fueron, y agotóse el río, secóse.
12 haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
Así el hombre yace, y no se tornará á levantar: hasta que no haya cielo no despertarán, ni se levantarán de su sueño.
13 “Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol )
¡Oh quién me diera que me escondieses en el sepulcro, que me encubrieras hasta apaciguarse tu ira, que me pusieses plazo, y de mí te acordaras! (Sheol )
14 In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
Si el hombre muriere, ¿[volverá] á vivir? Todos los días de mi edad esperaré, hasta que venga mi mutación.
15 Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
Aficionado á la obra de tus manos, llamarás, y yo te responderé.
16 Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
Pues ahora me cuentas los pasos, y no das tregua á mi pecado.
17 Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
Tienes sellada en saco mi prevaricación, y coacervas mi iniquidad.
18 “Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
Y ciertamente el monte que cae se deshace, y las peñas son traspasadas de su lugar;
19 yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
Las piedras son desgastadas con el agua impetuosa, que se lleva el polvo de la tierra: de tal manera haces tú perecer la esperanza del hombre.
20 Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
Para siempre serás más fuerte que él, y él se va; demudarás su rostro, y enviaráslo.
21 Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
Sus hijos serán honrados, y él no lo sabrá; ó serán humillados, y no entenderá de ellos.
22 Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”
Mas su carne sobre él se dolerá, y entristecerse ha en él su alma.