< Ayuba 14 >

1 “Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
“O homem, que nasce de uma mulher, é de poucos dias, e cheio de problemas.
2 Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
Ele cresce como uma flor, e é cortado. Ele também foge como uma sombra, e não continua.
3 Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
Você abre seus olhos para tal, e me levar a julgamento com você?
4 Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
Quem pode trazer uma coisa limpa de uma coisa impura? Nem um.
5 An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
Seeing seus dias estão determinados, o número de seus meses está com você, e você indicou seus limites que ele não pode passar.
6 Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
Desvie o olhar dele, para que ele possa descansar, até que ele cumpra, como um mercenário, seu dia.
7 “Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
“Pois há esperança para uma árvore se ela for cortada, que brotará novamente, que o seu ramo de oferta não cessará.
8 Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
Embora sua raiz envelheça na terra, e seu estoque morre no chão,
9 Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
yet através do cheiro da água, ela irá brotar, e brotam ramos como uma planta.
10 Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
Mas o homem morre, e é colocado em baixo. Sim, o homem desiste do espírito, e onde ele está?
11 Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
Como as águas falham a partir do mar, e o rio desperdiça e seca,
12 haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
para que o homem se deite e não se levante. Até que os céus não estejam mais acordados, nem serem despertados do sono.
13 “Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol h7585)
“Oh, que você me esconderia no Sheol, que você me manteria em segredo até que sua ira passasse, que você me indicaria um tempo determinado e se lembraria de mim! (Sheol h7585)
14 In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
Se um homem morrer, será que ele viverá novamente? Eu esperaria todos os dias da minha guerra, até minha liberação chegar.
15 Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
Você ligaria, e eu lhe responderia. Você teria um desejo pelo trabalho de suas mãos.
16 Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
Mas agora você conta meus passos. Você não cuida do meu pecado?
17 Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
Minha desobediência é selada em uma bolsa. Você prende minha iniqüidade.
18 “Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
“Mas a montanha que cai não dá em nada. A rocha é removida de seu lugar.
19 yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
As águas desgastam as pedras. As torrentes da mesma lavam o pó da terra. Assim você destrói a esperança do homem.
20 Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
Você prevalece para sempre contra ele, e ele parte. Você muda seu rosto, e o manda embora.
21 Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
Seus filhos vêm para honrar, e ele não sabe disso. Eles são trazidos para baixo, mas ele não percebe isso deles.
22 Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”
Mas sua carne tem dor, e sua alma dentro dele chora”.

< Ayuba 14 >