< Ayuba 14 >

1 “Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
女から生れる人は日が短く、悩みに満ちている。
2 Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
彼は花のように咲き出て枯れ、影のように飛び去って、とどまらない。
3 Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
あなたはこのような者にさえ目を開き、あなたの前に引き出して、さばかれるであろうか。
4 Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
だれが汚れたもののうちから清いものを出すことができようか、ひとりもない。
5 An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
その日は定められ、その月の数もあなたと共にあり、あなたがその限りを定めて、越えることのできないようにされたのだから、
6 Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
彼から目をはなし、手をひいてください。そうすれば彼は雇人のように、その日を楽しむことができるでしょう。
7 “Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
木には望みがある。たとい切られてもまた芽をだし、その若枝は絶えることがない。
8 Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
たといその根が地の中に老い、その幹が土の中に枯れても、
9 Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
なお水の潤いにあえば芽をふき、若木のように枝を出す。
10 Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
しかし人は死ねば消えうせる。息が絶えれば、どこにおるか。
11 Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
水が湖から消え、川がかれて、かわくように、
12 haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
人は伏して寝、また起きず、天のつきるまで、目ざめず、その眠りからさまされない。
13 “Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol h7585)
どうぞ、わたしを陰府にかくし、あなたの怒りのやむまで、潜ませ、わたしのために時を定めて、わたしを覚えてください。 (Sheol h7585)
14 In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
人がもし死ねば、また生きるでしょうか。わたしはわが服役の諸日の間、わが解放の来るまで待つでしょう。
15 Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
あなたがお呼びになるとき、わたしは答えるでしょう。あなたはみ手のわざを顧みられるでしょう。
16 Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
その時あなたはわたしの歩みを数え、わたしの罪を見のがされるでしょう。
17 Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
わたしのとがは袋の中に封じられ、あなたはわたしの罪を塗りかくされるでしょう。
18 “Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
しかし山は倒れてくずれ、岩もその所から移される。
19 yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
水は石をうがち、大水は地のちりを洗い去る。このようにあなたは人の望みを断たれる。
20 Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
あなたはながく彼に勝って、彼を去り行かせ、彼の顔かたちを変らせて追いやられる。
21 Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
彼の子らは尊くなっても、彼はそれを知らない、卑しくなっても、それを悟らない。
22 Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”
ただおのが身に痛みを覚え、おのれのために嘆くのみである」。

< Ayuba 14 >