< Ayuba 14 >

1 “Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
Man [that is] born of a woman [is] of few days, and full of trouble.
2 Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
He cometh forth like a flower, and is cut down: he fleeth also as a shadow, and continueth not.
3 Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
And dost thou open thy eyes upon such one, and bring me into judgment with thee?
4 Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
Who can bring a clean [thing] out of an unclean? not one.
5 An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
Seeing his days [are] determined, the number of his months [is] with thee, thou hast appointed his bounds that he cannot pass;
6 Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
Turn from him, that he may rest, till he shall accomplish, as a hireling, his day.
7 “Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
For there is hope of a tree, if it is cut down, that it will sprout again, and that its tender branch will not cease.
8 Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
Though its root shall become old in the earth, and its stock die in the ground;
9 Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
[Yet] through the scent of water it will bud, and bring forth boughs like a plant.
10 Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
But man dieth, and wasteth away: yes, man yieldeth his breath, and where [is] he?
11 Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
[As] the waters fail from the sea, and the flood decayeth and drieth up:
12 haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
So man lieth down, and riseth not: till the heavens [shall be] no more, they shall not awake, nor be raised out of their sleep.
13 “Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol h7585)
O that thou wouldst hide me in the grave, that thou wouldst keep me secret, until thy wrath is past, that thou wouldst appoint me a set time, and remember me! (Sheol h7585)
14 In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
If a man dieth, shall he live [again]? all the days of my appointed time will I wait, till my change shall come.
15 Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
Thou shalt call, and I will answer thee: thou wilt have a desire to the work of thy hands.
16 Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
For now thou numberest my steps: dost thou not watch over my sin?
17 Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
My transgression [is] sealed up in a bag, and thou sewest up my iniquity.
18 “Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
And surely the mountain falling cometh to naught, and the rock is removed out of its place.
19 yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
The waters wear the stones: thou washest away the things which grow [out] of the dust of the earth; and thou destroyest the hope of man.
20 Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
Thou prevailest for ever against him, and he passeth: thou changest his countenance, and sendest him away.
21 Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
His sons come to honor, and he knoweth [it] not; and they are brought low, but he perceiveth [it] not of them.
22 Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”
But his flesh upon him shall have pain, and his soul within him shall mourn.

< Ayuba 14 >