< Ayuba 14 >
1 “Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
Man that is born of a woman is of few days and full of trouble.
2 Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
He comes forth like a flower, and is cut down: he flees also as a shadow, and continues not.
3 Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
And does you open your eyes on such an one, and bring me into judgment with you?
4 Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
Who can bring a clean thing out of an unclean? not one.
5 An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
Seeing his days are determined, the number of his months are with you, you have appointed his bounds that he cannot pass;
6 Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
Turn from him, that he may rest, till he shall accomplish, as an hireling, his day.
7 “Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
For there is hope of a tree, if it be cut down, that it will sprout again, and that the tender branch thereof will not cease.
8 Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
Though the root thereof wax old in the earth, and the stock thereof die in the ground;
9 Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
Yet through the scent of water it will bud, and bring forth boughs like a plant.
10 Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
But man dies, and wastes away: yes, man gives up the ghost, and where is he?
11 Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
As the waters fail from the sea, and the flood decays and dries up:
12 haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
So man lies down, and rises not: till the heavens be no more, they shall not awake, nor be raised out of their sleep.
13 “Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol )
O that you would hide me in the grave, that you would keep me secret, until your wrath be past, that you would appoint me a set time, and remember me! (Sheol )
14 In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
If a man die, shall he live again? all the days of my appointed time will I wait, till my change come.
15 Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
You shall call, and I will answer you: you will have a desire to the work of your hands.
16 Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
For now you number my steps: do you not watch over my sin?
17 Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
My transgression is sealed up in a bag, and you sew up my iniquity.
18 “Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
And surely the mountains falling comes to nothing, and the rock is removed out of his place.
19 yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
The waters wear the stones: you wash away the things which grow out of the dust of the earth; and you destroy the hope of man.
20 Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
You prevail for ever against him, and he passes: you change his countenance, and send him away.
21 Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
His sons come to honor, and he knows it not; and they are brought low, but he perceives it not of them.
22 Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”
But his flesh on him shall have pain, and his soul within him shall mourn.