< Ayuba 14 >

1 “Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
Man born of a woman, living for a short time, is filled with many miseries.
2 Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
Who cometh forth like a flower, and is destroyed, and fleeth as a shadow, and never continueth in the same state.
3 Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
And dost thou think it meet to open thy eyes upon such an one, and to bring him into judgment with thee?
4 Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
Who can make him clean that is conceived of unclean seed? is it not thou who only art?
5 An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
The days of man are short, and the number of his months is with thee: thou hast appointed his bounds which cannot be passed.
6 Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
Depart a little from him, that he may rest, until his wished for day come, as that of the hireling.
7 “Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
A tree hath hope: if it be cut, it groweth green again, and the boughs thereof sprout.
8 Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
If its root be old in the earth, and its stock be dead in the dust:
9 Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
At the scent of water, it shall spring, and bring forth leaves, as when it was first planted.
10 Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
But man when he shall be dead, and stripped and consumed, I pray you where is he?
11 Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
As if the waters should depart out of the sea, and an emptied river should be dried up:
12 haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
So man when he is fallen asleep shall not rise again; till the heavens be broken, he shall not awake, nor rise up out of his sleep.
13 “Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol h7585)
Who will grant me this, that thou mayst protect me in hell, and hide me till thy wrath pass, and appoint me a. time when thou wilt remember me? (Sheol h7585)
14 In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
Shall man that is dead, thinkest thou, live again? all the days in which I am now in warfare, I expect until my change come.
15 Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
Thou shalt call me, and I will answer thee: to the work of thy hands thou shalt reach out thy right hand.
16 Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
Thou indeed hast numbered my steps, but spare my sins.
17 Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
Thou hast sealed up my offences as it were in a bag, but hast cured my iniquity.
18 “Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
A mountain falling cometh to nought, and a rock is removed out of its place.
19 yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
Waters wear away the stones, and with inundation the ground by little and little is washed away: so in like manner thou shalt destroy man.
20 Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
Thou hast strengthened him for a little while, that he may pass away for ever: thou shalt change his face, and shalt send him away.
21 Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
Whether his children come to honour or dishonour, he shall not understand.
22 Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”
But yet his flesh, while he shall live, shall have pain, and his soul shall mourn over him.

< Ayuba 14 >