< Ayuba 14 >

1 “Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
For a mortal born of a woman [is] short lived, and full of wrath.
2 Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
Or he falls like a flower that has bloomed; and he departs like a shadow, and cannot continue.
3 Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
Hast thou not taken account even of him, and caused him to enter into judgment before thee?
4 Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
For who shall be pure from uncleanness? not even one;
5 An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
if even his life should be [but] one day upon the earth: and his months are numbered by him: thou hast appointed [him] for a time, and he shall by no means exceed [it].
6 Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
Depart from him, that he may be quiet, and take pleasure in his life, [though] as a hireling.
7 “Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
For there is hope for a tree, even if it should be cut down, [that] it shall blossom again, and its branch shall not fail.
8 Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
For though its root should grow old in the earth, and its stem die in the rock;
9 Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
it will blossom from the scent of water, and will produce a crop, as one newly planted.
10 Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
But a man that has died is utterly gone; and when a mortal has fallen, he is no more.
11 Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
For the sea wastes in [length of] time, and a river fails and is dried up.
12 haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
And man that has lain down [in death] shall certainly not rise again till the heaven be dissolved, and they shall not awake from their sleep.
13 “Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol h7585)
For oh that thou hadst kept me in the grave, and hadst hidden me until thy wrath should cease, and thou shouldest set me a time in which thou wouldest remember me! (Sheol h7585)
14 In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
For if a man should die, shall he live [again], having accomplished the days of his life? I will wait till I exist again?
15 Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
Then shalt thou call, and I will hearken to thee: but do not thou reject the work of thine hands.
16 Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
But thou hast numbered my devices: and not one of my sins shall escape thee?
17 Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
An thou hast sealed up my transgressions in a bag, and marked if I have been guilty of any transgression unawares.
18 “Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
And verily a mountain falling will utterly be destroyed, and a rock shall be worn out of its place.
19 yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
The waters wear the stones, and waters falling headlong [overflow] a heap of the earth: and thou destroyest the hope of man.
20 Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
Thou drivest him to an end, and he is gone: thou settest thy face against him, and sendest him away;
21 Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
and though his children be multiplied, he knows [it] not; and if they be few, he is not aware.
22 Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”
But his flesh is in pain, and his soul mourns.

< Ayuba 14 >