< Ayuba 13 >
1 “Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
HE AQUÍ que todas estas cosas han visto mis ojos, y oído y entendido de por sí mis oídos.
2 Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
Como vosotros lo sabéis, lo sé yo; no soy menos que vosotros.
3 Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
Mas yo hablaría con el Todopoderoso, y querría razonar con Dios.
4 Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
Que ciertamente vosotros sois fraguadores de mentira; sois todos vosotros médicos nulos.
5 In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
Ojalá callarais del todo, porque os fuera sabiduría.
6 Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
Oid ahora mi razonamiento, y estad atentos á los argumentos de mis labios.
7 Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
¿Habéis de hablar iniquidad por Dios? ¿habéis de hablar por él engaño?
8 Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
¿Habéis de hacer acepción de su persona? ¿habéis de pleitear vosotros por Dios?
9 In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
¿Sería bueno que él os escudriñase? ¿os burlaréis de él como quien se burla de algún hombre?
10 Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
El os reprochará de seguro, si solapadamente hacéis acepción de personas.
11 Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
De cierto su alteza os había de espantar, y su pavor había de caer sobre vosotros.
12 Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
Vuestras memorias serán comparadas á la ceniza, y vuestros cuerpos como cuerpos de lodo.
13 “Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
Escuchadme, y hablaré yo, y véngame después lo que viniere.
14 Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
¿Por qué quitaré yo mi carne con mis dientes, y pondré mi alma en mi mano?
15 Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
He aquí, aunque me matare, en él esperaré; empero defenderé delante de él mis caminos.
16 lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
Y él mismo me será salud, porque no entrará en su presencia el hipócrita.
17 Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
Oid con atención mi razonamiento, y mi denunciación con vuestros oídos.
18 Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
He aquí ahora, si yo me apercibiere á juicio, sé que seré justificado.
19 Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
¿Quién es el que pleiteará conmigo? porque si ahora yo callara, fenecería.
20 “Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
A lo menos dos cosas no hagas conmigo; entonces no me esconderé de tu rostro:
21 Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
Aparta de mí tu mano, y no me asombre tu terror.
22 Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
Llama luego, y yo responderé; ó yo hablaré, y respóndeme tú.
23 Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
¿Cuántas iniquidades y pecados tengo yo? hazme entender mi prevaricación y mi pecado.
24 Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
¿Por qué escondes tu rostro, y me cuentas por tu enemigo?
25 Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
¿A la hoja arrebatada has de quebrantar? ¿y á una arista seca has de perseguir?
26 Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
¿Por qué escribes contra mí amarguras, y me haces cargo de los pecados de mi mocedad?
27 Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
Pones además mis pies en el cepo, y guardas todos mis caminos, imprimiéndolo á las raíces de mis pies.
28 “Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.
Y el [cuerpo mío] se va gastando como de carcoma, como vestido que se come de polilla.