< Ayuba 13 >
1 “Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
Mira, he visto todo esto con mis propios ojos, y lo he oído con mis propios oídos, y lo entiendo.
2 Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
Sé lo que sabes. No eres mejor que yo.
3 Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
Pero aun así me gustaría hablar con el Todopoderoso: ¡Quiero probarme ante Dios!
4 Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
En cuanto a ustedes, ¡encubren las cosas diciendo mentiras! ¡Todos ustedes son como los médicos que no pueden curar a nadie!
5 In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
¡Cuánto desearía que se callaran todos! Eso sería lo más sensato para ustedes.
6 Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
Escuchen mi argumento y presten atención a lo que tengo que decir.
7 Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
¿Creen que pueden decir mentiras para defender a Dios? ¿Hablan con engaño en su nombre?
8 Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
¿O es que quieren demostrar su favoritismo a Dios? ¿Argumentarán en favor de Dios?
9 In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
¿Concluirá Dios que hacen el bien cuando los examine? ¿Podrán engañarlo como si se tratara de un ser humano?
10 Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
¡No, definitivamente los reprenderá si le muestran secretamente su favoritismo!
11 Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
¿No les aterra su majestad? ¿Acaso no se paralizarían de miedo ante él?
12 Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
Sus dichos son tan útiles como la ceniza; sus argumentos tan débiles como el barro.
13 “Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
Callen y no me hablen. Déjenme hablar, pase lo que pase.
14 Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
Me hago responsable de mí mismo y estoy dispuesto a arriesgar mi vida.
15 Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
Aunque me mate, esperaré en él. Todavía seguiré defendiendo mis caminos ante él.
16 lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
Haciendo esto me salvaré, ya que ningún impío podría presentarse ante él.
17 Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
Escuchen atentamente lo que digo, y presten atención a mi explicación.
18 Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
Miren que he preparado mi caso y sé que se me dará la razón.
19 Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
¿Quién quiere discutir conmigo? Si se demuestra que estoy equivocado, estoy dispuesto a callar y morir.
20 “Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
Dios, tengo dos peticiones, entonces podré enfrentarme a ti.
21 Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
Deja de golpearme, y deja de aterrorizarme.
22 Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
Entonces llama, y yo responderé. O déjame hablar, y luego respóndeme.
23 Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
¿Cuáles son mis pecados e iniquidades? Muéstrame qué he hecho mal; ¿cómo me he rebelado contra ti?
24 Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
¿Por qué eres tan hostil conmigo? ¿Por qué me tratas como tu enemigo?
25 Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
¿Asustarías a una hoja movida por el viento o cazarías un pedazo de paja?
26 Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
Porque escribes cosas amargas contra mí y me haces pagar por los pecados de mi juventud.
27 Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
Pones mis pies en el cepo. Vigilas cada uno de mis pasos. Incluso inspeccionas mis huellas.
28 “Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.
Me deshago como algo podrido, como ropa apolillada.